Ana Tunkarar Zabukan 2027, Shugaban INEC Ya Dauki Sabon Alkawari ga Ƴan Najeriya
- Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC ya ce kuri’un masu zabe za su yi tasiri a zaben gwamnan jihar Ekiti
- Farfesa Josh Amupitan ya ce yawan masu rajistar zabe a jihar ya haura miliyan daya yayin da zaben zai gudana a watan gobe
- Hukumar ta gargadi jam’iyyu da masu zabe kan sayen kuri’u yayin da Amupitan ya bada tabbacin INEC za ta yi adalci a zaben
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Ekiti - Shugaban hukumar INEC, Farfesa Josh Amupitan, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa kuri’un da za a kada ne kawai za su yi tasiri a zaben gwamnan Ekiti.
Farfesa Amupitan ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar tantance shirye-shiryen zabe da ya kai jihar Ekiti tare da sauran kwamishinonin INEC kafin zaben gwamna da za a gudanar ranar 20 ga watan Yuni.

Source: Twitter
Shugaban INEC ya ziyarci jihar Ekiti
A yayin taron, shugaban INEC ya kuma gabatar da kundin rajistar masu kada kuri’a ga jam’iyyun siyasa kamar yadda Daily Trust ta rahoto.
Shugaban INEC ya bayyana muhimmancin rajistar masu kada kuri’a wajen tabbatar da cewa an gudanar da sahihin zabe
Amupitan ya bayyana taron a matsayin wani abu mai matukar muhimmanci ga hukumar, yana mai cewa ba kasafai ake samun jihar da za ta karbi bakuncin shugaban INEC tare da kusan dukkan kwamishinonin kasa ba.
Ya ce dokar zabe ta tanadi cewa dole ne a wallafa tare da gabatar da kundin masu kada kuri’a ga jam’iyyun siyasa kwanaki 30 kafin gudanar da zabe.
A cewarsa, cikin manyan ayyuka tara da hukumar ta tsara domin zaben, an kammala guda bakwai, yayin da za a kammala yakin neman zabe ranar 18 ga watan Yuni.
Yawan masu rajistar zabe a jihar Ekiti ya karu
Farfesa Amupitan ya bayyana cewa an samar da kundin masu kada kuri’a ne bayan tattara bayanai da tantancewa mai zurfi domin tabbatar da sahihancinsa.
Ya ce yawan masu rajistar zabe a jihar Ekiti ya karu sosai bayan gudanar da rajistar katin zabe ta dindindin watau CVR, in ji rahoton Vanguard.
A cewarsa, daga kusan masu zabe 900,000 da jihar ke da su a baya, yanzu adadin ya kai kimanin mutum 1,059,360.
Ya kara da cewa INEC ba za ta iya gudanar da sahihin zabe ita kadai ba, saboda hakan na bukatar hadin kan jam’iyyun siyasa da sauran masu ruwa da tsaki.

Source: Original
INEC ta aika sako ga jam’iyyun siyasa
Shugaban hukumar ya bukaci jam’iyyun siyasa su wayar da kan magoya bayansu domin fitowa su kada kuri’a a ranar zabe.
Ya sake jaddada cewa kuri’un jama’a za su yi tasiri, yana mai buga misali da yadda ake tura sakamakon zabe kai tsaye ta hanyar RVP a zabukan baya.
Amupitan ya kuma nuna damuwa kan matsalar sayen kuri’u, yana mai bayyana hakan a matsayin babban kalubale ga dimokuradiyyar Najeriya.

Kara karanta wannan
"Za su yi amfani"; Shugaban INEC ya ba masu kada kuri'a tabbaci kan zabe a Najeriya
Babu sunan PDP a rajistar zaben Ekiti
A wani labari, mun ruwaito cewa, INEC da jam'iyyun siyasa na ci gaba da shirye-shiryen zaben gwamnan jihar Ekiti, wanda za a gudanar a watan Yunin 2026.
Rahoto ya tabbatar da cewa INEC ta fitar da jerin sunayen 'yan takara 12 da mataimakansu, wadanda za su fafata a zaben gwamnan Ekiti.
Sai dai abin da ya ja hankali shi ne rashin ganin sunan dan takarar gwamnan PDP da mataimakinsa, wanda ake ganin yana da alaka da rikicin jam'iyyar.
Asali: Legit.ng

