Shugaba Tinubu Ya Amince da Sabon Aikin N46bn a Kano
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da ware Naira biliyan 46 domin sake shimfiɗa da kuma gina titin saukar jiragen sama na biyu a filin jirgin saman Kano
- Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce aikin zai ƙara inganta ayyukan filin jirgin tare da ɗaga martabarsa a duniya
- Gwamnatin tarayya ta kuma fara aikin inganta tashar aikin Hajji a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano da ke birnin Kano
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Kano - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ware Naira biliyan 46 domin gyara tashar jirgin sama ta Malam Aminu Kano (MAKIA).
Shugaba Tinubu ya amince da kudaden ne domin sake shimfiɗa da kuma sake gina titin saukar jiragen sama na biyu a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano.

Source: Facebook
Tashar Channels tv ta ce Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da sabuwar tashar cikin gida ta Muhammadu Adamu Dankabo da aka gyara tare da inganta ta a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano ranar Talata, 28 ga watan Yulin 2026.
A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan yaɗa labarai da sadarwa, Tunde Moshood, ya fitar, ministan ya ce aikin na daga cikin manyan shirye-shiryen da gwamnatin Shugaba Tinubu ke aiwatarwa domin bunƙasa harkokin sufurin jiragen sama.
Keyamo ya bayyana muhimmancin filin jirgin Kano
Festus Keyamo ya ce gwamnatin tarayya ta ware filin jirgin saman Kano domin samun manyan ayyukan ingantawa saboda muhimmancinsa ga tattalin arziki da harkokin sufuri.
Ya kuma ce hakan ne ya sa Shugaba Tinubu ya naɗa tsohon gwamnan Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, a matsayin shugaban hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya (FAAN).
“Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ware filin jirgin saman Kano domin manyan ayyukan ingantawa saboda muhimmancin wannan filin jirgin."
“Shugaban ƙasa ya amince da ware Naira biliyan 46 domin sake shimfiɗa da kuma sake gina titin saukar jiragen sama na biyu, domin filin jirgin saman Kano ya iya gogayya da sauran manyan filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa.”
- Festus Keyamo

Source: Facebook
Gwamnati ta fara inganta tashar Hajji
Ministan ya sake jaddada kudirin gwamnatin tarayya na sauya fasalin harkokin sufurin jiragen sama a ƙarƙashin ajandar Renewed Hope ta Shugaba Tinubu.
Ya bayyana cewa Kano na da muhimmanci sosai ga tattalin arzikin Najeriya, yana mai cewa birnin shi ne cibiyar kasuwancin Arewacin Najeriya, jaridar Leadership ta kawo labarin.
“Filin jirgin saman Mallam Aminu Kano shi ne zuciyar kasuwancin Arewacin Najeriya. Saboda haka muka ware Kano domin samun manyan ayyukan ingantawa.”
- Festus Keyamo
Tinubu ya yabawa Umahi
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya taya Ministan Ayyuka, David Umahi, murnar cika shekara 63 da haihuwa a duniya.

Kara karanta wannan
Fadar shugaban kasa ta hango kura kurai a kalaman Obi, ta yi masa zazzafan martani
Shugaba Bola Tinubu ya yaba da jajircewarsa wajen aiwatar da ayyukan more rayuwa masu ɗorewa a faɗin tarayyar Najeriya.
Mai girma Bola Tinubu ya yabawa Umahi kan ƙwazonsa, sadaukar da kai ga aiki, da kuma kishin ƙasa da yake nunawa wajen gudanar da ayyukansa.
Asali: Legit.ng

