NDC: Mai Neman Takarar Sanata Ya Maka INEC da Jam'iyyarsu Kwankwaso a Kotu

NDC: Mai Neman Takarar Sanata Ya Maka INEC da Jam'iyyarsu Kwankwaso a Kotu

  • Isaac Nwachukwu ya kai ƙarar NDC da INEC kotu, yana neman a amince da shi a matsayin ɗan takarar sanata na Imo ta Arewa
  • Mai neman takarar ya yi ikirarin cewa ya biya N25m ga NDC domin sayen fom da kuma tallafi ga jam’iyyar, amma daga baya aka cire sunansa
  • Nwachukwu ya yi zargin cewa an sauya sunansa da na wani ɗan takara na daban duk da cewa an riga an amince da shi kuma an karbi kudinsa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Imo – Wani mai neman tikitin Sanata a mazabar Imo ta Arewa a ƙarƙashin NDC, Isaac Nwachukwu, ya kai ƙarar jam’iyyar da hukumar INEC a gaban babbar kotun tarayya da ke Owerri.

Nwachukwu na neman kotun ta tabbatar da shi a matsayin halastaccen ɗan takarar sanata na jam’iyyar domin shiga zaɓen shekarar 2027.

Kara karanta wannan

Sun yi laifi: Kotu ta ci tarar tsohon gwamna da jam'iyyar ADC Naira miliyan 1

Wani mai neman takarar sanata ya maka jam'iyyar NDC da INEC a kotu a Imo
Tutar jam'iyyar NDC, inda Kwankwaso da Obi za su yi takara a 2027. Hoto: @iamHSDickson
Source: Facebook

Nwachukwu ya maka NDC da INEC a kotu

A cikin ƙarar da ya shigar, Nwachukwu ya yi zargin cewa an hana shi tikitin jam’iyyar duk da cewa ya cika dukkan sharuɗɗan da aka gindaya masa, in ji rahoton Punch.

Ya ce bayan ya samu amincewar sauran masu neman takarar a matakin sulhu na tsayar da ɗan takara, daga baya aka cire sunansa tare da maye gurbinsa da wani mutum.

Isaac Nwachukwu ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 25 ga jam’iyyar domin neman tikitin takarar.

A cewarsa, Naira miliyan 20 daga cikin kuɗin tallafi ne ga jam’iyyar, yayin da Naira miliyan 5 kuma kuɗin sayen fom ɗin takara ne na kujerar sanatan Imo ta Arewa.

Abubuwan da yake nema a gaban kotu

Ya kuma ce ya halarci tantancewar da jam’iyyar ta shirya kuma an amince da shi a matsayin wanda ya cancanci shiga zaɓen fidda gwani.

Kara karanta wannan

Yadda Amaechi yake fuskantar matsin lamba kan zama abokin takarar Atiku a ADC

Nwachukwu ya yi zargin cewa an samu kura-kurai a tsarin gudanar da zaɓen fitar da gwani, inda aka ware kuɗin da ya biya aka sanya sunan wani ɗan takara mai suna Matthew Omegara.

Daga cikin buƙatun da ya gabatar wa kotu akwai neman a ayyana shi a matsayin zaɓaɓɓen ɗan takarar NDC na mazabar Imo ta Arewa.

Haka kuma yana son kotun ta hana jam’iyyar NDC tsayar da wani ɗan takara daban a zaɓen sanata na yankin, in ji rahoton Leadership.

Bugu da ƙari, ya nemi kotun ta umarci INEC da kada ta amince da takarar wani mutum a madadinsa har sai an kammala shari’ar.

Dan siyasar yana neman kotu ta ayyana a matsayin halastaccen dan takarar jam'iyyar ADC.
Harabar babbar kotun tarayya da ke babban birnin tarayya Abuja. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Ba a ji ta bakin INEC, NDC ba

A cikin takardar rantsuwar da ya gabatar, Nwachukwu ya ce bayan an amince da shi a matsayin ɗan takara na sulhu kuma aka saka sunansa cikin jerin waɗanda suka yi nasara, daga baya aka maye gurbinsa da wani ɗan takara ba tare da bin ƙa’idojin jam’iyyar da dokar zaɓe ba.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, jam’iyyar NDC da INEC ba su fitar da wata sanarwa dangane da zarge-zargen da Nwachukwu ya yi a gaban kotu ba.

Kara karanta wannan

Janar Rabe: Buratai ya yi gargadi kan 'sace' gwamnoni da ministoci a Najeriya

Martanin Kwankwaso kan dokar NDC

A wani labari, mun ruwaito cewa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya tofa albarkacin bakinsa kan sabuwar dokar da jam'iyyar NDC ta bullo da ita.

'Dan takarar mataimakin shugaban kasar a zaben 2027 ya nuna cewa dokar abu ne wanda suka dade suna magana a kai.

Dokar dai mai neman hana 'yan siyasa sauya sheka bayan cin zabe ba ta shafi Peter Obi da madugun na Kwankwasiyya ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com