Ana Wata ga Wata: Shugaban Ƙaramar Hukuma Ya Nada Hadimi a Bangaren Rawa

Ana Wata ga Wata: Shugaban Ƙaramar Hukuma Ya Nada Hadimi a Bangaren Rawa

  • Shugaban ƙaramar hukumar Kuje, Danjuma Shekwolo, ya naɗa wani matashi a matsayin hadiminsa a bangaren rawa
  • Takardar naɗin ta ce an ba Danladi mukamin ne saboda jajircewa, ƙwazo da gudummawar da ya bayar wajen ci gaban ƙaramar hukumar Kuje
  • Shekwolo ya ce an samu kuskuren fahimta, yana mai jaddada cewa mukamin da aka ba Danladi shi ne mataimaki na musamman kan harkokin nishaɗi, ba rawa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Shugaban ƙaramar hukumar Kuje da ke Babban Birnin Tarayya Abuja, Danjuma Shekwolo, ya ba da mamaki bayan wani nadin hadimi da ya yi.

Shekwolo ya naɗa Ibrahim Danladi a matsayin mataimaki na musamman bangaren rawa domin shakatawa.

Wani ciyaman ya nada hadimi a bangaren rawa
Taswirar birnin Abuja da ke tsakiyar Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Takardar naɗin ta fito ne da kwanan watan 13 ga Yuli kuma ta fara aiki nan take, cewar rahoton TheCable.

Kara karanta wannan

Remi Tinubu ta lallaba Saudiyya, tana so a taimaka wa Najeriya kan karatun allo

Takardar mai lamba KAC/CHM/30/VOL.1 ta bayyana cewa an ba Danladi wannan mukami ne saboda ƙwazo, sadaukarwa, jajircewa da gudummawar da ya bayar wajen bunƙasa ƙaramar hukumar Kuje.

A cikin takardar, shugaban ya buƙaci sabon mataimakin ya tabbatar da amincewar da aka nuna masa ta hanyar gudanar da ayyukansa cikin gaskiya da ƙwazo domin amfanin al'umma.

Takardar ta bayyana mukamin a matsayin Mataimaki na Musamman kan Rawa, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce bayan ya bazu a kafafen yaɗa labarai.

Ciyaman ya nada matashi hadiminsa kan rawa
Hadimin shugaban karamar hukuma, Ibrahim Danladi da ministan Abuja, Nyesom Wike. Hoto: @frankulom, Govwike.
Source: Twitter

Sai dai da yake magana da manema labarai, Shekwolo ya musanta cewa ya naɗa mataimaki kan rawa kawai, yana cewa an yi kuskuren fahimtar abin da mukamin yake nufi.

Ya ce ainihin mukamin da aka ba Danladi shi ne Mataimaki na Musamman kan Harkokin Nishaɗi, ba mataimaki kan rawa ba kamar yadda wasu suka ruwaito.

An tuna cewa Shekwolo, ɗan takarar APC, ya lashe zaɓen shugaban ƙaramar hukumar Kuje a watan Fabrairu bayan samun ƙuri'u 17,269, inda ya kayar da Zakwoyi Danlami na PDP wanda ya samu ƙuri'u 15,824.

Shugaban ya bayyana fatansa cewa sabon mataimakin zai cika burin gwamnatin ƙaramar hukumar ta hanyar gudanar da aikinsa yadda ya dace da kuma ba da gudummawa ga ci gaban Kuje.

Kara karanta wannan

Yaki da yunwa: Oluremi ta fadi yadda Tinubu ya tallafa wa yan kasa da abinci

An tuna cewa Shekwolo, ɗan takarar APC, ya lashe zaɓen shugaban ƙaramar hukumar Kuje a watan Fabrairu bayan samun ƙuri'u 17,269, inda ya kayar da Zakwoyi Danlami na PDP wanda ya samu ƙuri'u 15,824.

Shugaban ya bayyana fatansa cewa sabon mataimakin zai cika burin gwamnatin ƙaramar hukumar ta hanyar gudanar da aikinsa yadda ya dace da kuma ba da gudummawa ga ci gaban Kuje.

Ciyaman ya nada hadimai 100 a Rivers

A baya, kun ji cewa shugaban karamar hukumar Obio-Akpor a jihar Rivers, Chijioke Ihunwo ya yi abin a yaba kan nadin mukamai da ya yi a ofishinsa.

Ihunwo ya nada akalla masu ba shi shawara na musamman guda 100 da za su taimaka masa a shugabancinsa lamarin da ya jawo maganganu.

Shugaban karamar hukumar ya bukaci sababbin masu mukaman da su tabbatar da yin aiki tukuru a jihar domin samar da shugabanci nagari.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.