Kano da Wasu Jihohin Arewa 11 Za Su Fuskanci Tsananin Zafi, NiMet Ta Yi Gargadi

Kano da Wasu Jihohin Arewa 11 Za Su Fuskanci Tsananin Zafi, NiMet Ta Yi Gargadi

  • Hukumar NiMET ta fitar da gargaɗi kan hauhawar zafi wanda zai iya haifar da cututtuka a sassa daban-daban na ƙasar Najeriya
  • Yanayin zafin zai iya kai wa maki 45°C a arewacin ƙasar, tare da barazanar bullar cutar sankarau, musamman a jihohin Arewa 12
  • Wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa Najeriya na ɗaya daga cikin ƙasashen da za su fuskanci matsanancin zafi zuwa 2050

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Abuja - Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta fitar da sanarwar gargaɗi ga ɗaukacin ƙasar nan game da ƙaruwar yanayin zafi.

NiMet ta yi gargaɗin cewa tsananin zafin da ake ciki zai iya haifar da matsananciyar matsala ga mutane sakamakon dumamar jiki da zafin zai haifar a sassa da dama na ƙasar.

NiMet ta yi hasashen cewa za a samu tsananin zafi a wasu jihohin Arewacin Najeriya
Wasu da ake kyautata zaton Musulmai a wajen Mauludi ana tsananin zafi. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Jihohin Arewa 12 da za su fuskanci tsananin zafi

Kara karanta wannan

Jira ya kare, Gwamnan Adamawa zai nuna ɗan takarar da yake so ya gaje shi a 2027

A cikin wata sanarwar da NiMet ta fitar, hukumar ta ce ƙaruwar yanayin zafin a faɗin Najeriya na iya kai wasu ga shiga yanayin galabaita saboda zafi, musamman a wasu jihohin Arewa, in ji rahoton BBC Hausa.

Jihohin da NiMet ta bayyana cewa suna cikin hadari na wannan tsananin zafin sun haɗa da:

  1. Neja
  2. Kebbi
  3. Sokoto
  4. Zamfara
  5. Katsina
  6. Kano
  7. Yobe
  8. Jigawa
  9. Bauchi
  10. Gombe
  11. Borno
  12. Adamawa

A cewar sanarwar, sauran jihohin da ba a ambata ba ma na iya fuskantar tasirin zafin, ciki har da sassan kudancin ƙasar.

A hasashen NiMet, yanayin zafin zai iya kai wa maki 40 zuwa 45 a ma'aunin salshiyas a arewacin ƙasar, yayin da tsakiyar ƙasar kuma zai kai tsakanin maki 35 zuwa 38 a ma'aunin salshiyas, a Kudancin ƙasar kuma yanayin na iya kai wa maki 33 zuwa 35.

Hanyoyin kare kai daga galabaitar zafi

NiMet ta buƙaci mazauna wadannan jihohi da su ɗauki matakan kariya domin rage haɗarin kamuwa da cututtukan da zafi ke haifarwa, in ji rahoton The Guardian.

Hukumar ta ce kasancewar ƙura a sararin samaniya a sassan arewa, idan aka haɗa da matsanancin zafi, zai ƙara haɗarin galabaitar jiki, bugun zafi, da kuma yiwuwar ɓullar cutar sankarau.

Kara karanta wannan

Oshiomhole ya nemi Tinubu ya soke lasisin MTN da wasu kamfanonin Afrika ta Kudu

NiMet ta ba da shawarar cewa:

"A rika shan ruwa sosai sannan a zauna a wuraren da ke da isasshen iska ko na'urar sanyaya ɗaki idan hakan ta sawwaka, a guji cinkoso a wuraren da ba su da iska, sannan a rage zama ƙarƙashin rana kai-tsaye".
Hukumar NiMet ta bukaci 'yan Najeriya su dage da shan ruwa saboda guje wa cututtukan zafi.
Wata mata tana shan ruwan roba yayin da rana ta take. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Kariya ga yara da masu bukata ta musamman

Hukumar ta kuma ba da shawarar sanya hula, gilashin kariya daga rana, da kuma shafa man kariya yayin da ake waje, tare da zaɓar tufafi marasa nauyi waɗanda ke ba da damar shigar iska.

NiMet ta buƙaci iyaye da masu kula da yara da su tabbatar da cewa jarirai suna cikin sanyi da kuma isasshen ruwa, sannan ta yi gargaɗin cewa kada a taɓa barin yara a cikin motocin da aka faka.

Bugu da ƙari, an shawarci mazauna yankunan da su rage ayyukan motsa jiki kuma su zauna a cikin gida lokacin da zafi ya fi tsananta, musamman tsakanin ƙarfe 12:00 na rana zuwa 4:00 na yamma.

Kara karanta wannan

Kaduna da wasu jihohin Najeriya za su samu ruwan sama yau Litinin in ji NiMet

Wani bincike na Jami'ar Oxford ya nuna Najeriya na ɗaya daga cikin ƙasashen da za su fuskanci matsanancin zafi nan da shekarar 2050.

Kankara ta zama zinare saboda zafi

A wani labari, mun ruwaito cewa, matsanancin zafin da aka taba tafkawa a jihar Bauchi ya sanya kankara tafi komai daraja a cikin kayan abubuwan da ake amfani da su don neman sauki.

Wani mutumi da ya ke sana'ar sayar da kankarar ya ce a kullum yana samun ribar N30,000 saboda yadda mutane ke dandazon sayen kankarar.

Matsanancin zafin ya sanya kankara tana wahala, kuma ta zama tamkar zinare, domin kuwa yadda ake nemanta ba a neman kayan marmari da sauran abubuwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com