Abuja
Ɓangaren PDP na Seyi Makinde ya ziyarci Atiku, Obi da Kwankwaso na ADC a Abuja yau Alhamis, 9 ga Afrilu, 2026, yayin da tsagin Wike ya musanta taron yau.
A labarin nan, za a ji wata babbar kotu da ke zamanta a Abuja ta kawo ƙarshen shari'ar gwamnatin tarayya da wasu ƴan Boko Haram da aka gurfanar a gabanta.
Gwamnatin Amurka ta ce rashin tsaro ya karu a Najeriya, za ta kwashe jami'anta a Abuja. Bayan turo sojoji ta yi gargadi kan zuwa wasu jihohin Najeriya.
Wasu manyan jami'an gwamnati a Najeriya sun taba yi wa 'yan jarida barazana. Wasu daga cikinsu sun fito sun nemi afuwa bayan sun fuskanci matsin lamba.
Hasashen yanayi na Laraba, 8 ga Afrilu, 2026 ya nuna za a yi kura a Arewa da ruwan sama a Kudu, tare da gargaɗin direbobi da matafiya su kiyaye yau.
Manyan attajirai irin su Aliko Dangote da kamfanin NNPCL sun yi alkawarin bada Naira biliyan N30.5 domin tallafa wa shirin yaƙi da yunwa na Sanata Remi Tinubu yau.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Dalhatu Abubakar a matsayin shugaban hukumar kula da kasuwanci a Najeriya tare da sabon kwamitin gudanarwa.
Dan kasar Amurka, Alex Barbir ya sanar da fita daga Najeriya. Ya yi magana ga Sheikh Gumi da Bashir Ahmad. Bashir ya ce korar shi da kasar nan aka yi.
Gwamnoni da 'yan majalisar APC sun fara kira da a ba su tikitin takara kai tsaye yayin da wasu gwamnonin da suka gama suke neman tikitin takarar Sanata.
Abuja
Samu kari