Peter Obi ko Kwankwaso: NDC Ta Shirya Tsaida 'dan Takarar Shugaban Kasa a Zaben 2027

Peter Obi ko Kwankwaso: NDC Ta Shirya Tsaida 'dan Takarar Shugaban Kasa a Zaben 2027

  • Jam’iyyar NDC za ta gudanar da babban taro na musamman a Abuja domin tabbatar da Peter Obi a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen 2027
  • Peter Obi ya zama ɗan takara taya tilo da ya nuna sha'awa sakamakon babu wani da ya sayi fom ɗin neman takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NDC
  • Shugabannin jam’iyyar sun bayyana cewa an tantance Obi tare da amincewa da cancantarsa kafin taron tabbatar da shi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Jam’iyyar adawa ta NDC ta sanar da cewa za ta gudanar da babban taro na musamman a ranar Asabar, 30 ga watan Mayu, domin tsaida dan takarar shugavan kasa.

NDC ta ce taron zai tabbatar da tsohon gwamnan jihar Anambra kuma dan takarar LP a zaben 2027, Peter Obi, a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar NDC ta jawo Kabiru Marafa, ta ba shi tikitin takarar gwamnan Zamfara a 2027

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa an shirya gudanar da taron ne a babban birnin tarayya Abujayau Asabar.

Ana sa ran shugabannin jam’iyya NDC daga kowane mataki, wakilai daga jihohi daban-daban da magoya baya za su hallara domin nuna goyon baya ga takarar Obi.

NDC ta tabbatar da shirinta

Sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar NDC, Osa Director, ya tabbatar da wannan ci gaba a wata tattaunawa da jaridar The Nation a Abuja.

A cewarsa, jam’iyyar ta kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin gudanar da taron cikin lumana da tsari.

Ya bayyana cewa taron zai kasance wata muhimmiyar alama a tafiyar siyasar jam’iyyar gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

Yadda Peter Obi ya zama ɗan takara shi kaɗai

Rahotanni sun nuna cewa Peter Obi ne kaɗai ya sayi fom ɗin nuna sha’awa da kuma neman takarar shugaban ƙasa a karkashin jam’iyyar NDC.

Saboda haka, babu wani ɗan takara da zai fafata da shi a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar, lamarin da ya sa ya zama ɗan takara guda ɗaya da ke neman tikitin shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan

Bayan kotu ta share wa Jonathan hanya, PDP ta buɗe masa ƙofar komawa Aso Villa

Wannan ya bai wa jam’iyyar damar shirya taron musamman domin tabbatar da shi kai tsaye a matsayin wanda zai jagoranci tutar NDC a zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa.

Kwamitin tantancewa ya amince da shi

Kafin wannan mataki, kwamitin tantance ‘yan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar karkashin jagorancin Sanata Sam Egwu ya gayyaci Peter Obi domin tantancewa.

Bayan gudanar da aikin tantancewar, kwamitin ya bayyana cewa Obi ya cika dukkan sharuddan da jam’iyyar ta gindaya ga masu neman tikitin shugaban ƙasa.

Hakan ne ya sa aka amince da shi tare da ba shi damar shiga matakin tabbatarwa ba tare da wata matsala ba.

Ana sa ran karin bayani

Ana sa ran shugabannin jam’iyyar NDC za su fitar da karin bayanai kan taron da kuma shirye-shiryen yakin neman zaɓen 2027 bayan kammala taron tabbatar da Peter Obi a Abuja.

Masu sa ido kan harkokin siyasa na kallon wannan mataki a matsayin wani muhimmin ci gaba a shirye-shiryen jam’iyyar domin fafatawa da manyan jam’iyyun siyasa a babban zaɓen da ke tafe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: