Latest
Wata kotu a ƙasar Iran ta yanke wa mawakin nan, Amir Hossein Maghsoudloo hukuncin kisa bayan kama shi da laifin taɓa mutuncin Annabi Muhammad SAW.
Adadin mutanen da suka rasu sakamakon iftila'in fashewar tankar mai ya karu a jihar Neja. Mutane kusan 100 sun rasu yayin da wasu da dama suka jikkata.
Abu Radde da Umar Black sun mika wuya tare da sakin fursunonin da suka tsare bayan matsin lambar sojoji. An ce sojoji sun rufe hanyoyin da 'yan ta'adda za su tsere.
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta yi nasarar hallaka 'yan bindiga 7 yayin da suka gwabza da 'yan ta'adda a Katsina. An ceto yara 207 a hannun masu safarar mutane.
Hadimin shugaban ƙasa, Taiwo Oyedele ya ce nan da watan Maris ake sa ran kudirorin canza fasalin haraji za su zama doka, za a fara aiwatarwa a Yuli.
An gudanar da jana'izar mutum 86 daga cikin wadanda suka mutu a gobarar tankar man fetur a jihar Neja yayin da wasu 'yan kasuwa suka rasa dukiyoyinsu.
Kamfanin TCN ya bayyana cewa dole sai jama'a sun taimaka masu wajen sa ido a kan kare kayayyakin wutar lantarki daga bata gari da su ke kawo nakasu ga aikinsu.
Gwamnan jihar Yobe ya raba tallafin kudi ga wasu talakawa masu aikin saran itace, matafiya da masu aikin titi. Gwamnan ya raba kudin ne yayin ziyarar ba zata.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya tafi zuwa kasar Switzerland domin halartar taro kan tattalin arzikin duniya. Ya samu rakiyar jami'an gwamnati.
Masu zafi
Samu kari