A Karshe, Hatsabiban Shugabannin 'Yan Bindiga Sun Ajiye Makamansu, Sun Mika Wuya

A Karshe, Hatsabiban Shugabannin 'Yan Bindiga Sun Ajiye Makamansu, Sun Mika Wuya

  • Hatsabiban shugabannin 'yan bindiga, Abu Radde da Umar Black sun mika, sun saki fursunoni bayan matsin lamba daga sojoji
  • An rahoto cewa sojojin Operation Fansan Yanma sun karya lagon ‘yan ta’adda, sun kulle hanyoyin tserewar miyagun a Arewa
  • Majiyoyi sun tabbatar da cewa Abu Radde da Umar Black sun hakura da ta’addanci ne bayan hare-haren sojoji da ya hana su sakat

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Katsina - Wasu hatsabiban shugabannin 'yan ta’adda, Abu Radde da Umar Black sun ajiye makamanssu tare da mika wuya a Katsina.

Rahotanni sun bayyana cewa Abu Radde da Umar Black sun dade suna kai hare-hare da sace mutane a garuruwan Batsari da Safana.

Rahotanni sun bayyana cewa shugabannin 'yan ta'adda 2 sun mika wuya a Katsina
Wasu shugabannin 'yan ta'adda sun mika wuya a Katsina, sun saki wadanda suka sace. Hoto: @ZagazOlaMakama
Asali: Twitter

Zagazola Makama, masani kan harkokin tsaro da yaki da ‘yan tawaye a Tafkin Chadi, ya bayyana hakan a rahotonsa na kafar X.

Kara karanta wannan

Sojoji su na ragargaza, an kai samamen dare a maboyar Boko haram

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugabannin 'yan bindiga sun mika wuya

An ce shugabannin 'yan ta'addan sun kuma saki dukkanin mutanen da suka yi garkuwa da su yayin da suka mika wuya.

Hakazalika, sun mika wuya ne bayan hare-haren sojoji karkashin Operation Hadarin Daji da Operation Forest Sanity a yankin Arewa maso Yamma.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa sojoji sun tsananta hare-hare kan dabar Abu Radde da Umar Black wanda ya tilasta 'yan ta'addar mika wuya.

Rahoto ya ce 'yan ta'addar sun mika manyan makaman da suke aiki da su da suka hada da bindigogi tare da sakin mutane da suke tsare a sansaninsu.

Sojoji sun tsananta hare-hare kan 'yan bindiga

Wannan ci gaban ya biyo bayan karfafa ayyukan sojoji a Arewa maso Yamma, inda suke ci gaba da kai farmaki mai karfi kan sansanonin ‘yan ta’adda.

Hare-haren sama da na kasa sun jefa ‘yan ta’adda cikin rudani, wanda ya tilasta su tserewa cikin firgici daga sansaninsu tare da neman mafaka.

Kara karanta wannan

IPOB ta sako Sheikh Gumi a gaba bayan shawarsa a kan ta'addanci

Rahotanni sun bayyana cewa manyan shugabannin 'yan ta’adda a Arewa sun tarwatse, kuma babu alamar za su iya sake hadewa saboda hare-haren sojoji.

Sojoji sun rufe hanyar tserewar 'yan ta'adda

An ce sojojin Najeriya sun kulle dukkanin wasu hanyoyin da 'yan ta'addar za su iya bi domin tserewa daga hare-haren.

Hakazalika, sojoji sun lalata hanyoyin samar da kayayyaki ga 'yan ta’addan, wanda ya kara raunana karfinsu na kai hare-hare a jihohin Arewa maso Gabas.

Wadannan nasarorin sun kara tabbatar da kudurin sojojin Najeriya na kawo karshen ta’addanci da mayar da zaman lafiya ga al’ummomin Arewa.

Bello Turji ya kafa sansani a Zamfara

A wani labarin, mun ruwaito cewa Bello Turji, fitaccen shugaban ‘yan bindiga, ya kafa sabon sansani a jihar Zamfara, bayan hare-haren sojoji.

Kafa sabon sansanin ya biyo bayan farmakin sojoji da ya jefa tawagar Turji cikin mummunan yanayi a Fakai da Shinkafi, inda suka tarwatse.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga 30 sun shiga har cikin daki sun sace mata da miji a Abuja

Rahotanni sun ce sansanin zai taimaka wajen kula da wadanda suka ji rauni da kuma tsare fursunonin da aka sace daga hare-hare.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.