Gwamnoni 3 Sun Zauna a Gida, ba Su Halarci Tantancewar APC gabanin Zaben 2027 ba

Gwamnoni 3 Sun Zauna a Gida, ba Su Halarci Tantancewar APC gabanin Zaben 2027 ba

  • Jam'iyyar APC ta tabbatar da cewa gwamnoni uku ba su samu halartar tantancewar shirin tunkarar babban zaben 2027
  • Shugaban APC na kasa, Farfesa Nentwe Yilwatda ya ce gwamnonin sun bada uzuri kuma za a tantance su a duk lokacin da suka shirya
  • Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da takwaransa na jihar Katsina, Malam Dikkko Radda na cikin wadanda aka tantance zuwa yanzu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Gwamnonin jam'iyyar APC uku ba su samu damar halartar wurin tantancewar da aka gudanar yau Asabar, 10 ga watan Mayu, 2026.

Kwamitin tantancewa da APC ta kafa karkashin jagorancin shugaban jam'iyyar na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya fara tantance gwamnonin a wani bangare na shirin 2027.

Shugaban APC.
Shugaban APC na kasa, Farfesa Nentwe Yilwatda a wurin tantance yan takarar jam'iyya mai mulki Hoto: @OfficialAPCNig
Source: Twitter

Sai dai, rahoton da The Cable ta wallafa yau Asabar ya nuna cewa gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara; gwamnan Ebonyi, Francis Nwifuru; da gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ba su halarci tantancewar ba.

Kara karanta wannan

Pantami ya bayyana muhimmancin zaben fitar da gwani ga jam'iyyar APC, ya yi gargadi

Me yasa gwamnoni 3 ba su halarta ba?

Da yake magana yayin gudanar da aikin, Shugaban APC, Farfesa Yilwatda ya ce gwamnonin uku sun nemi afuwa ne saboda wasu harkokin gwamnati da suka taso a jihohinsu.

“Gwamnonin uku da ba su bayyana ba, duk sun bayar da dalilan rashin zuwansu,” in ji shi.

Ya kara da cewa kasancewarsu shugabannin zartarwa na jihohinsu ya sa aka ba su damar zuwa a lokacin da suka samu dama.

“Gwamnan Kwara ya ce yana da harkokin gwamnati, mun ba shi uzuri. Gwamnan Ebonyi ma haka, haka kuma gwamnan Rivers,” in ji shugaban APC.

Yaushe APC za ta tantance gwamnonin?

Yilwatda ya bayyana cewa APC za ta ci gaba da tantance gwamnonin duk lokacin da suka samu damar halarta.

“Mun ce su shugabanni ne kuma kwamandoji a jihohinsu. Duk lokacin da suka samu dama su kira kwamitin tantancewa, za mu ba su wuri su zo a lokacin da ya dace da su,” in ji shi.

Kara karanta wannan

Kallo ya koma sama yayin da APC ta tantance gwamnoni 14 babu sunan Fubara

Gwamnonin da suka halarta

Daga cikin gwamnonin da aka tantance akwai Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, Muhammadu Inuwa Yahaya na Gombe, Nasir Idris na Kebbi, Caleb Mutfwang na Plateau da Hyacinth Alia na Benue.

Sauran sun hada da Sheriff Oborevwori na Delta, Umar Bago na Neja, Dauda Lawal na Zamfara, Bassey Otu na Cross River da Ahmed Aliyu na Sokoto.

Gwamnoni.
Shugaban APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda lokacin kaddamar da kwamitin tantance gwamnoni Hoto: @OfficialAPCNig
Source: Twitter

Wannan tantancewa wani bangare ne na shirye-shiryen da APC ke yi domin tunkarar babban zaben 2027.

Jam'iyyar ta fara tattaunawa da tantancewa ta cikin gida musamman gwamnonin da ke kan mulki da kuma manyan masu ruwa da tsaki domin gane irin karfin da take da shi kafin 2027, in ji rahoton Guardian.

APC ta tara fiye da Naira biliyan 4

A wani labarin, kun ji cewa jam’iyyar APC ta samu sama da Naira biliyan 4.45 daga sayar da fam ga wadanda ke neman takarar kujerar gwamna a 2027.

Kara karanta wannan

"Mu kece raini": Gwamnan Gombe ya yi martani bayan kafiyar Pantami da Goje

Bayanai sun nuna cewa APC ta samu Naira miliyan 200 daga Shugaba Bola Tinubu da Stanley Osifo, waɗanda suka sayi fam.ɗin neman takarar shugaban ƙasa.

Haka kuma, APC ta sayar da fam ɗin gwamna kan Naira miliyan 50, na.Sanata kan Naira miliyan 20, yayin da na ɗan majalisar wakilai ya kai Naira miliyan 10.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262