Isra'ila Ta Yi wa Trump Kunnen Uwar Shegu, Ta Kaddamar da Sababbin Hare Hare

Isra'ila Ta Yi wa Trump Kunnen Uwar Shegu, Ta Kaddamar da Sababbin Hare Hare

  • Kasar Isra'ila ta kai sababbin hare-haren sama a kudancin Lebanon duk da cewa Shugaba Donald Trump ya yi gargadi a kan irin wannan matakin
  • Donald Trump ya gargadi Benjamin Netanyahu da ya nuna taka-tsantsan kan rikici da Lebanon, yana mai cewa an dade ana yakin Hezbollah
  • Iran dai ta fito ta gargadi Isra’ila cewa ci gaba da hare-hare ko mamaye yankunan Lebanon zai saba wa sabuwar yarjejeniyar da aka kulla

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Lebanon - Isra'ila ta kai sababbin hare-hare a kudancin Lebanon, duk da sukar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi kan matakan da Tel Aviv ke dauka a yankin.

Rahotanni sun nuna cewa a ranar Laraba, jiragen yakin Isra'ila sun kai hare-hare a yankin Nabatieh al-Fawqa da kuma wajen garin Kfar Tebnit da ke makwabtaka da shi.

Kara karanta wannan

'Ni ne gatan Isra'ila': Trump ya fusata da lamarin Netanyahu a yaki da Iran

Isra'ila ta kai sababbin hare-hare zuwa Lebanon duk da Trump ya yi suka kan hakan.
Hayaki na tashi daga wani yanki na Kudancin Lebanon sakamakon harin Isra'ila. Hoto: Abbas FAKIH / AFP via Getty Images
Source: Getty Images

Trump ya gargadi Netanyahu kan Hezbollah

Rahoton BBC ya nuna cewa an kai harin ne a wasu wurare da ake zargin mayakan Hezbollah ke amfani da su, ko da yake rundunar sojin Isra'ila ba ta fitar da wata sanarwa kai tsaye kan sabon harin ba.

A ranar Talata, Donald Trump ya bayyana cewa ya kamata Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya kasance mai taka-tsantsan wajen tafiyar da rikicin Lebanon.

Da yake magana yayin taron kungiyar G7 a Faransa, Trump ya ce:

"Isra'ila ta dade tana fada da Hezbollah, kuma mutane da yawa na ci gaba da rasa rayukansu."

Ya kuma bayyana cewa bai gamsu da wani hari da Isra'ila ta kai a baya ba, yana mai cewa harin ya yi yawa fiye da yadda ya kamata.

Trump ya kara da cewa dangantakarsa da Netanyahu tana da kyau, amma hakan ba ya hana shi bayyana ra'ayinsa idan ya ga wani mataki da bai dace ba.

Kara karanta wannan

Bayan sulhu da Iran, Trump ya soki Netanyahu, ya zarge shi da babban laifi

Hare-hare sun ci gaba duk da yarjejeniyar Iran

Tun bayan sanar da yarjejeniyar sulhu tsakanin Amurka da Iran a daren Lahadi, Isra'ila da Hezbollah suka ci gaba da musayar hare-hare, in ji rahoton Yahoo News.

A ranar Lahadi din, wani hari da Isra'ila ta kai a Beirut bayan harba rokoki daga Lebanon ya kara jefa tattaunawar sulhun cikin wani mummunan yanayi.

Rahotanni sun nuna cewa Pakistan, wadda ke taka rawa a matsayin mai shiga tsakani, ta ce yarjejeniyar da ake kokarin kammalawa ta kunshi batun Lebanon.

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi dai ya gargadi cewa kasarsa za ta dauki duk wani sabon hari da Isra'ila za ta kai a Lebanon ko ci gaba da kasancewar sojojinta a yankin a matsayin karya yarjejeniyar wucin gadi da aka cimma da Amurka.

A ranar Juma'a ne ake sa ran Iran da Amurka za su rattaba hannu kan yarjejeniyar sulhu.
Shugaban Amurka, Donald Trump (hagu) da Ministan wajen Iran, Abbas Araghchi (dama) Hoto: Anna Moneymaker / ATTA KENARE via Getty Images
Source: Getty Images

Ranar rattaba hannu kan yarjejeniyar

Ma'aikatar harkokin wajen Switzerland ta bayyana cewa ana sa ran Amurka da Iran za su rattaba hannu kan yarjejeniyar a ranar Juma'a a garin Bürgenstock.

Kara karanta wannan

Duk da cika bakin Amurka kan sulhu, Iran ta ja mata layi, ta gindaya sharuɗa

Trump ya ce zai iya gudanar da taron manema labarai domin karanta yarjejeniyar gaba daya ga duniya.

Ya kuma yi ikirarin cewa yarjejeniyar za ta hana Iran mallakar makamin nukiliya, tare da bude mashigar ruwa ta Hormuz domin harkokin kasuwanci ba tare da wata matsala ba.

Zargin amfani da sinadari mai guba a Lebanon

A wani labari, mun ruwaito cewa, Rundunar sojin Isra’ila ta yi amfani da wani sinadari mai guba wanda zai iya yin matuƙar illa a wuraren da jama’a ke zaune a Lebanon.

An ga hayaki na musamman da ke fitowa daga irin wannan makami har zuwa ranar 30 ga Mayun 2026 a Nabatieh, wani birni mai mutane 40,000.

Sauran bidiyoyin da aka tabbatar da sahihancinsu sun nuna cewa an yi amfani da sinadarin a kusa da birnin Tyre da ke bakin teku da wasu garuruwa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com