Hukumar Hisbah Ta Dakatar da Wani Babban Biki a Yobe, An Cafke Ɗan TikTok a Kano
- Hukumar Hisbah ta dakatar da wani bikin 'Colour Festival' da wasu matasa suka shirya, tana mai cewa ya saɓa wa koyarwar addinin Musulunci
- Hukumar ta gargaɗi cewa za ta ɗauki matakin doka kan duk wanda ya shirya ko ya goyi bayan ayyukan da take ganin sun saɓa wa ƙa'idodin Musulunci
- A Kano kuma, Hisbah ta kama wani fitaccen ɗan TikTok, Namadina Tudunwada, kan zargin ƙarfafa zina ta hanyar bidiyon da ya wallafa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da takwas a aikin jarida
Yobe - Hukumar Hisbah ta jihar Yobe, reshen Damaturu, ta sanar da dakatar da wani bikin "Colour Festival" da wasu matasa suka shirya gudanarwa a babban birnin jihar.
Hukumar ta ce ta ɗauki matakin ne domin kare tarbiyya, kiyaye ƙa'idodin addinin Musulunci da kuma hana ayyukan da take ganin sun saɓa wa koyarwar addini.

Source: Facebook
Hisbah ta hana wani biki a Yobe
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami'in yaɗa labarai na rundunar Hisbah ta Damaturu, Y. M. Abba, ya fitar a ranar Litinin, in ji rahoton Punch.
Sanarwar ta ce hukumar za ta ci gaba da sa ido tare da ɗaukar matakan da suka dace domin tabbatar da zaman lafiya, tarbiyya da kuma kare ƙa'idodin addini a cikin al'umma.
Hisbah ta kuma gargaɗi mutane da ƙungiyoyi da su guji shirya bukukuwa ko tarukan da suka saɓa wa koyarwar Musulunci.
Ta ƙara da cewa duk wanda aka samu da shirya ko tallafa wa irin waɗannan ayyuka zai fuskanci hukunci bisa tanadin doka.
Sai dai sanarwar ba ta yi cikakken bayani kan irin bikin "Colour Festival" da aka dakatar ba, kuma ba a samu wata hujja mai zaman kanta da ta tabbatar da cikakkun bayanansa ba.
Hisbah ta kama ɗan TikTok a Kano
A wani labarin makamancin haka, Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama fitaccen mai ƙirƙirar bidiyoyin TikTok, Namadina Tudunwada, bisa zargin ya yi kalaman da za su iya ƙarfafa matasa su aikata zina.
Rahoton Daily Post ya nuna cewa mataimakin babban kwamandan Hisbah, Mujahid Aminuddeen, ya ce an kama Namadina ne bayan wani bidiyo da ya wallafa ya bazu a kafafen sada zumunta.
A cikin bidiyon, an ce Namadina ya kwatanta kuɗin yin aure da kuɗin zina, inda ya ce zina na iya cin kusan N2,000, yayin da yin aure zai iya kai kusan N200,000.

Source: UGC
Hisbah ta ce irin wannan kwatanci na iya sa wasu matasa su guji aure tare da karkata zuwa ayyukan da suka saɓa wa tarbiyya, kamar yadda muka ruwaito.
Hukumar ta ce za ta ci gaba da gudanar da cikakken bincike kafin yanke hukuncin matakin doka da za a ɗauka a kansa.
Hisbah ta kafawa masu Keke-Napep doka
A wani labari, mun ruwaito cewa, Hisbah ta Kano ta haramta tsarin daukar mata da direbobin adaidaita sahu ke tana mai cewa ya saɓa wa koyarwar Musulunci.
Hukumar Hisbah ta sanar da umarnin ne yayin ganawa da shugabannin BOTORA, inda suka tattauna hanyoyin inganta tsari.
Ta kuma buƙaci haɗin kai wajen yaƙi da satar yara, fataucin miyagun ƙwayoyi da rashin ɗa’a, yayin da BOTORA ta yi alƙawarin bin umarnin.
Asali: Legit.ng


