An Fitar da Jerin Kasashe 50 da Trump Ya Laftawa Wasu Kudi, ciki har da Najeriya

An Fitar da Jerin Kasashe 50 da Trump Ya Laftawa Wasu Kudi, ciki har da Najeriya

  • Gwamnatin Amurka ta mayar da shirin biyan lamunin biza na dala 20,000 dindindin ga matafiya daga kasashe 50 da suka hada da Najeriya
  • Shirin zai shafi wasu masu neman bizar kasuwanci da yawon bude ido, inda za a mayar musu da kudin idan sun bi sharuddan zama a Amurka
  • Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce biyan lamunin ba ya tabbatar da samun biza, kuma za a biya ne kawai idan jami'in ofishin jakadanci ya bayar da umarni

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Washington DC – Gwamnatin Amurka ta sanar da mayar da shirin biyan lamunin biza na dala 20,000 dindindin ga matafiya daga kasashe 50, ciki har da Najeriya da wasu kasashen Afirka 29.

Sabuwar dokar za ta shafi wasu masu neman bizar B1/B2 ta kasuwanci da yawon bude ido, inda jami'in ofishin jakadanci zai iya umartar su da su biya lamunin kafin a ba su bizar shiga kasar.

Kara karanta wannan

Karfin hali: Yadda aka kama mutum 2 da zargin cefanar da filayen gwamnatin Kano

Shugaba Donald Trump
Shugaba Donald Trump zai shiga jirgi ya yi tafiya. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Punch ta rahoto cewa Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta wallafa a ranar Juma'a, tana mai cewa shirin zai taimaka wajen tabbatar da bin dokokin shige da fice.

Yadda shirin lamunin biza zai gudana

A cewar gwamnatin Amurka, duk matafiyin da ya bi sharudan bizar kuma ya fice daga kasar kafin wa'adin zamansa ya cika, za a mayar masa da kudin lamunin.

Ma'aikatar ta ce jami'an jakadanci na iya bukatar masu neman biza su biya lamunin da zai kai dala 20,000 kafin a ba su izinin tafiya.

Ta kara da cewa shirin gwajin da aka fara a shekarar 2025 ya nuna cewa tsarin yana taimakawa wajen tabbatar da cewa masu biza suna bin dokokin shige da fice na Amurka.

Jerin kasashen da abin ya shafa

Vanguard ta wallafa cewa sabuwar dokar ta shafi kasashe 50 a fadin duniya yayin da guda 30 suka kasance daga nahiyar Afrika;

Kara karanta wannan

An kama dan shekara 20 da zargin ba 'yan bindiga makamai

  1. Algeria
  2. Angola
  3. Antigua and Barbuda
  4. Bangladesh
  5. Benin
  6. Bhutan
  7. Botswana
  8. Burundi
  9. Cabo Verde
  10. Cambodia
  11. Central African Republic
  12. Côte d'Ivoire
  13. Cuba
  14. Djibouti
  15. Dominica
  16. Ethiopia
  17. Fiji
  18. Gabon
  19. The Gambia
  20. Georgia
  21. Grenada
  22. Guinea
  23. Guinea-Bissau
  24. Kyrgyz Republic
  25. Lesotho
  26. Malawi
  27. Mauritania
  28. Mauritius
  29. Mongolia
  30. Mozambique
  31. Namibia
  32. Nepal
  33. Nicaragua
  34. Nigeria
  35. Papua New Guinea
  36. São Tomé and Príncipe
  37. Senegal
  38. Seychelles
  39. Tajikistan
  40. Tanzania
  41. Togo
  42. Tonga
  43. Tunisia
  44. Turkmenistan
  45. Tuvalu
  46. Uganda
  47. Vanuatu
  48. Venezuela
  49. Zambia
  50. Zimbabwe
Shugaba Donald Trump
Donald Trump yayin magana a wajen taro a Amurka. Hoto: Getty Images
Source: Facebook

Jirgin yaki ya yi hatsari a Amurka

A wani labarin, mun ruwaito cewa wani jirgin yakin F-35B na rundunar sojin ruwa ta Amurka ya yi hatsari tare da kama wa da wuta a yankin jihar California.

Matukin jirgin ya samu damar amfani da na'urar ceto kafin jirgin ya fadi, kuma an kai shi asibiti inda likitoci suka tabbatar cewa raunukan da ya samu ba su da hadarin rasa rai.

Jami'an kashe gobara sun garzaya wurin domin kashe wutar da ta tashi bayan hatsarin, yayin da ake ci gaba da binciken musabbabin afkuwar lamarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng