Siyasar Najeriya
Manyan shugabannin jam’iyyar Democratic Party uku da dan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar SDP a jihar Abia sun koma jam’iyyar All Progressives Congress.
Kungiyoyin makiyaya ‘yan Arewa sun yi watsi da dokar hana kiwo a fili da gwamnonin kudu suka kafa, suna masu bayyana ta a matsayin wani nau'i na tsoratarwa.
Wasu mambobin jam'iyyar Peoples Democratic Party sun shawarci jam'iyyar da ta bi a hankali game da batun raba tikitin takarar shugaban kasa a babban zaben 2023.
Rikicin ya barke ne bayan dakatar da shugaban marasa rinjaye, Hon. Anyadike Nwosu, da wasu ‘yan majalisa biyar da kakakin majalisar, Paul Emezim yayi a yau.
Har yanzun akwai sauran rikici tsakanin Gwamnan Kwara da ministan yaɗa labarai da al'adu, amma a halin yanzun, uwar jam'iyyar APC ta ƙasa ta shiga lamarin.
Biyo bayan saɓanin da aka samu tsakanin gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq da ministan yaɗa labarai, APC tace zata duba lamarin kuma zata yi hukunci.
Yerima ya ce zai tsaya takarar shugaban kasa a 2023 duk da matsayar da kungiyar Gwamnonin Kudu suka dauka a baya-bayan nan na ganin sun mallaki wannan kujerar.
Kungiyar Ohanaeze Ndigbo ta bukaci kungiyar gwamnonin kudu da su amincewa yankin kudu maso gabas ta samar da Shugaban kasa domin a samu damar buga wasa da kyau.
A wasu yan kwanaki da suka gabata gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da sallamar masu bada shawara na musamman banda mutum ɗaya, da alama ta yi amai ta lashe.
Siyasar Najeriya
Samu kari