Siyasar Najeriya
Jami'an hukumar EFCC sun sha dakyar a hannun 'yan daba a jihar Kaduna a lokacin da suka zo kama wani da ake zargin yana saen kuri'un jama'a a wurin zaben nan.
Hyacinth Alia, dan takarar jam'iyyar gwamna na Jam'iyyar All Progressives Congress (APC) a Benue ya lallasa takwararsa na PDP a akwatunan zaben gidan gwamnati.
Jam'iyyar PDP na baiwa jam'iyya mai mulki mamaki a sakamakon zaben rumfuma biyu da suka fito daga gidan gwamnatin Kaduna, Isah Ashiru ya samu nasara kan Sani.
Rahoton da muke samo daga jihar Legas na bayyana yadda hukumar zabe ta INEC ta bayyana dage zaben gwamna da 'yan majalisun jihohi zuwa wani lokacin na daban.
Ga dukkan alamamu hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa INEC ta shawo kan matsalar rashin ɗora sakamakon zabe da na'urar BVAS wanda ya jawo cece kuce a baya.
Wasu mutane cikin masu zabe wani gari mai suna Garam, a karamar hukumar Tafa da ke Jihar Niger sun ce sun gwammace a basu abinci a maimakon a tura musu kudi.
Wani bidiyo ya nuna yadda wani kwamishinan jihar Bauchi ya fito yana raba kudi gabanin zaben gwamna da aka yi a yau Asabar, an bayyana yadda lamarin ya faru.
Kawo yanzun, rahoton da muka samu daga yankin ƙaramar hukumar Rimin Gado ya nuna cewa akalla akwatunan zaɓe 10 wasu yan daba suka lalata a mazabu daban-daban.
Bayan tsaikon da aka samu sakamakon rashin saita na'urorin BVAS, a yau Asabar, 18 ga watan Maris, 2023 ake gudanar da zaben gwamnoni da yan majalisar jihohi.
Siyasar Najeriya
Samu kari