Yan fashi
Rahoton da aka tattara kan hare-haren yan bindiga musamman a yankin arewa maso yamma, ya nuna cewa maharan sun hallaka sojoji 10 da kuma wasu mutum 21 a mako.
Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya gargaɗi alkalan jihar katsin da kuma mambobin ƙungiyar Lauyoyi kan tsayawa nemanrwa yan ta'addan da aka kame beli.
Hukumar kwastam ta ƙasar nan, reshen jihar Katsina dake arewa maso yammacin Najeriya, tace ta kwace jarkokin man fetur sama da 1000 da ake kaiwa yan bindiga.
Jami'an yan sanda reshen babban birnin tarayya Abuja, sun yi ram da wasu mutum biyu da suke zargin na aikin kaiwa yan bindiga kayayyakin Abinci a yankin Kuje.
Miyagun 'yan bindiga sun sace shugaban ƙungiyar matasa (NYCN) reshen ƙaramar hukumar Odogbolu, jihar Ogun, sun nemi 'yan uwa su tattara musu miliyan N-30m.
Tun bayan katse hanyoyin sadarwa a jihar Katsina, yan bindiga sun cigaba da cin karen su babu babbaka kasancewar mutane basu da hanyar neman ƙarin jami'ai.
Wasu 'yan fashi da makami sun dira wani coci a Abuja, sun dabawa mai gadi wuka inda suka shiga suka fara binciken neman kudi a cikin cocin na Dunamis da Abuja.
Wata kawar dan sanatan da aka hallaka a jihar Kaduna ta bayyana wasu abubuwan da suka faru kafin mutuwarsa. Ta ce an shiga gidansa kafin mutuwarsa da wata biyu.
Kwamishinan 'yan sanda ya ba da umarnin gaggawa cewa, dole ne jami'ai su nemo wadanda suka kashe dan sanata Bala Ibn Na-Allah. Ya bukaci jama'a su ba da hadin k
Yan fashi
Samu kari