Jihar Rivers
Shugaban riko na jihar Rivers, Ibok-Ete Ibas, ya tabo batun gayyatar Gwamna Siminalayi Fubsra wanda aka dakatar domin fara bincikensa kan mukaman da ya nada.
Jam’iyyar PDP a Ondo ta koka kan matsaloli inda ta yi barazanar neman dokar ta-baci idan Gwamna Aiyedatiwa ya kasa magance matsalar tsaro ba da ke addabar al'umma.
Majalisar wakilai ta kafa kwamiti mai mutane 21 domin lura da harkokin majalisar dokokin Rivers da aka dakatar. Kwamitin zai lura da aikin da shugaban riko ke yi.
Mata a Rivers sun fito kan tituna suna zanga zangar goyon bayan gwamnatin Tinubu kan dakatar da gwamna Simi Fubara da ya yi. Sun ce an samu zaman lafiiya a jihar.
Jagoran 'yan Neja Delta, Thomas Ekpemupolo Tompolo ya ce yana kokarin sansanta rikicin jihar Rivers tsakanin Simi Fubara da Wike. Ya ce Fubara zai dawo kujerarsa.
Tsohon dan majalisar wakilai, Farah Dagogo ya bayyana rashin jin dadin yadda shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da zababben gwamnan jihar Ribas.
Bayan saba umarninta, wata kotun tarayya da ke Port Harcourt ta bukaci shugaban mulkin jihar Ribas ya bayyana dalilin da yasa ya nada shugabannin kananan hukumomi.
Gwamnonin PDP daga Adamawa, Enugu, Osun, Oyo, Bauchi, Akwa Ibom, Plateau, Delta, Taraba, Zamfara da Bayelsa sun shigar da Bola Tinubu kara kan dokar ta-ɓaci a Rivers
Shugaban rikon jihar Rivers, Ibok-Ete Ekwe Ibas ya nada shugabannin riko a kananan hukumomi 23 duk da kotu ta hana shi. Kotu ta hana shi cigaba da yin nade nade.
Jihar Rivers
Samu kari