Bayan Ya Ƙi Barin PDP, an Taso Gwamna Dauda a Gaba kan Dokar Ta Ɓaci a Zamfara

Bayan Ya Ƙi Barin PDP, an Taso Gwamna Dauda a Gaba kan Dokar Ta Ɓaci a Zamfara

  • NDYC ta bukaci gwamnatin tarayya ta ayyana dokar ta baci a Zamfara saboda yawaitar kashe-kashe da tabarbarewar tsaro da doka
  • Kungiyar ta ce lamarin ya kai matakin da ake rasa tsaro kwata-kwata, mazauna yankin ke rayuwa cikin tsoro da fargabar rasa rayuka
  • Sannan kungiyar NDYC ta jaddada cewa tun da aka ayyana dokar ta baci a Jihar Rivers, ya kamata a yi gaggawa a yi irinsa a Zamfara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Yenagoa, Bayelsa - Kungiyar 'Niger Delta Youth Congress' (NDYC) ta tura bukata ga gwamnatin tarayya kan jihar Zamfara.

Kungiyar ta bukaci ayyana dokar ta-baci a jihar Zamfara saboda yawaitar tashin hankali da rashin tsaro.

An taso gwamnan Zamfara a gaba kan dokar ta-ɓaci
An kuma bukatar Bola Tinubu ya sanya dokar ta-ɓaci a Zamfara. Hoto: Dauda Lawal, Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Twitter

Zamfara: An roki Tinubu ya sanya dokar ta-ɓaci

A wata sanarwa da shugaban kungiyar na kasa, Israel Uwejeyan, ya sanya wa hannu, NDYC ta ce satar mutane da kashe-kashe sun yi kamari, cewar Leadership.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kungiyar ta kwatanta lamarin da yadda gwamnatin tarayya ta hanzarta ayyana dokar ta baci a jihar Rivers, inda ta ce ya dace a Zamfara.

NDYC ta ce rikicin da ke faruwa a jihar Zamfara yana barazana ne ga rayuwar jama’a, inda al’ummomi ke zaune cikin tsananin tsoro.

Kungiyar ta bayyana cewa murabus da tsohon Sufeto-Janar na ‘yan sanda, MD Abubakar, ya yi daga hukumar tsaron jihar ya nuna gazawar gwamnati.

Dalilan da ake bukatar sanya dokar ta-ɓaci a Zamfara
Kungiya ta roki Tinubu ya sanya dokar ta-ɓaci a Zamfara. Hoto: Dauda Lawal.
Asali: Facebook

Dalilan neman sanya dokar ta-ɓaci a Zamfara

Har ila yau, NDYC ta ce akwai rikici na siyasa a jihar, majalisar dokokin jihar ta rabu gida biyu, kuma ana rikici tsakanin ‘yan majalisa.

NDYC ta ce idan ana ganin rikicin siyasa ya sa aka ayyana dokar ta-ɓaci a Rivers, to, rikicin Zamfara ya fi cancanta a dauki matakin.

Kungiyar ta bukaci Shugaba Bola Tinubu da Majalisar Tsaro ta kasa da su gaggauta ayyana dokar ta baci a Zamfara ba tare da bata lokaci ba.

Sanarwar ta ce:

“Muna rokon Shugaban kasa da Majalisar Tsaro ta kasa da su ayyana dokar ta baci a Zamfara ba tare da bata lokaci ba.
"Irin gaggawar da aka nuna a jihar Rivers ya kamata a nuna ita ma a Zamfara, kasa da haka nuna wariya ne.
"Muna tare da duk ‘yan Najeriya da ke fuskantar rashin tsaro ko a Arewa, Kudu, Gabas ko Yamma. Amma muna bukatar adalci.

Kungiyar ta ce abin takaici ne yadda ake nuna bambanci inda ake fifita wasu yankunan fiye da wasu a Najeriya.

Ƙungiyar ta ce:

"Niger Delta ba za ta amince a ci gaba da nuna bambanci ba, inda wasu yankuna ake fifitasu, wasu kuma ana nunawa karfi."

An bukaci Tinubu ya sanya dokar ta-ɓaci a Zamfara

Kun ji cewa wata ƙungiyar Arewa ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya ayyana dokar ta-baci a jihar Zamfara saboda tabarbarewar tsaro.

Kungiyar CAJ ta zargi gwamnatin Zamfara da mulkin kama karya yayin da ta ce jihar ba ta samun wani ci gaba a yanzu.

NCAJ ta ce garuruwa sun koma biyan haraji ga ‘yan bindiga, jami’an gwamnatin jihar na amfana da haramtacciyar hakar ma’adinai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.