Sauki Ya Zo: Matatar Dangote Ta Yi Rangwame a Farashin Man Fetur da Dizal a Najeriya

Sauki Ya Zo: Matatar Dangote Ta Yi Rangwame a Farashin Man Fetur da Dizal a Najeriya

  • Matatar Dangote da ke jihar Legas ta sauke farashin kowace litar man fetur daga N1,215 zuwa N1,165 a Najeriya domin saukaka wa mutane
  • Rahotannin da suka fito yau Laraba, 5 ga watan Agusta, 2026 sun ce an rage farashin dizal daga N1,650 zuwa N1,570 kan kowace lita
  • Sabon sauyin ya nuna raguwar N50 a fetur da N80 a dizal, wanda ake ganin wata alama ce da samun sauki ga yan Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Legas, Nigeria - Matatar Dangote da ke jihar Legas a Kudu maso Yammacin Najeriya ya yi sabon rangwwme a kan farashin man fetur (PMS) da man dizan domin rage wa jam's radadi.

Matatar hamshakin dan kasuwar kuma wanda ya fi kowa arziki a Afirka ta rage farashin da take bai wa yan kasuwa sarin fetur daga N1,215 zuwa N1,165 kan kowace lita.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya yi magana da limaman Katolika suka cire tsoro, sun ja da Tinubu

Fetur.
Yadda ake hada hadar man fetur a gidan mai a Najeriya Hoto: Anadolu
Source: Getty Images

Wata majiya mai tushe da ta nemi a sakaya sunanta ce ta tabbatar wa Tribune Online cewa matatar ta kuma rage farashin dizal (AGO) daga N1,650 zuwa N1,570 kan kowace lita.

Dangote ya rage farashin fetur da dizal

Sabon sauyin ya nuna an rage farashin fetur da N50 a kowace lita, yayin da aka rage farashin dizal da N80 a kowace lita.

Ana sa ran ƙarin bayanai za su fito nan gaba kan sabon tsarin farashin da sauran bayanan da suka shafi wannan sauyi.

Ku saurari karin bayani....

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262