Jihar Legas
Wani gini a yankin Ebute Metta da ke birnin Lagas ya kama gobara kimanin sa'o'i 48 bayan wata gobara ta afku a yankin Balogun. Hotunan afkuwar lamarin ya nuna cewa gobarar ta kama ne ba da wasa ba, domin an gano hayaki na tashi.
Hankula sun tashi jiya yayin da jirgin sama mai lamba rijista JQ2324 da ya tashi daga Legas zuwa Abuja ya fara hayaki a sama. An gano cewa, jirgin na kamfanin Azman na dauke da fasinjoji 120 ne kuma dole ce tasa ya koma filin...
Kungiyar kare hakkin musulmai a ranar Laraba ta zargi wani mutum mai suna Alex Chukwugo da laifin garkuwa da mutane, fyade da kuma dirkawa wata yarinya bahaushiya mai shekaru 18 ciki. Kungiyar MURIC tayi ikirarin cewa, Chukwugo...
Wani mutumi mai aikin wanki da guga a jahar Legas, Blessing Demian yana neman agaji tare da namen kai masa dauki bayan wani dansanda ya dirka masa harsashi a kafarsa kawai saboda yana soyayya da budurwar abokin Dansandan.
Rahotanni sun tabbatar da mutuwar tsohon gwamnan jahar Legas na mulkin Soja na farko, Birgediya Mobolaji Olofunso Johnson mai ritaya a ranar Laraba, 30 ga watan Oktoban shekarar 2019.
Ko kun san cewa ana daukowa masu kudin Najeriya mata daga kasar Amurka su zo su dinga yi musu rawa? Eh wannan gaskiya ne, da yawa daga cikin 'yammatan sun je an canja musu halittarsu domin su kara kyau domin jawo hankalin mazan...
An kai wa hukumar EFCC karar zargin Jigon APC Bola Tinubu. Yanzu dai ana so EFCC ta binciki inda Tinubu ya samo kudi a lokacin zaben Shugaban kasa bayan an samu motocin kudi a gidansa.
Wani mummunan bala'i ya auku a birnin Ikko na jihar Legas yayin da ajali ya katse hanzarin wani mutum yana tsaka da sassarfa a kan hanyar WEMCO da ke yankin Ogba da sanyin safiyar ranar Lahadin da ta gabata.
Tattalin arzikin Najeriya ya karu a watanni shidan farko na bana, a cewar wani rahoto da Hukumar Kididdiga ta Kasa, NBS ta wallafa a kan adadin kudaden shida da jihohi 36 na kasar da kuma garin Abuja suka tara.
Jihar Legas
Samu kari