Karatun Ilimi
Gwamnatin tarayya ta ce za ta gina wata makarantar sakandare ta zamani a Abuja, wacce za a kashe naira biliyan 1.7 wajen gina ta, kuma a cikin shekara daya.
Hukumar NDLEA ta ce rahoton da wani jami'in ta ya fitar na cewa kaso 60% cikin 100% na daliban Kano na shan kwayoyi ba gaskiya ba ne, ta ce kuskure aka samu.
Masana harkokin ilimi sun fitar da wasu muhimman dalilai da suka sa ilimi ya gaza a Najeriya musamman a makarantun firamare da yara ba sa iya karatu.
Umar Audu, dan jarida mai bincike ta karkashin kasa ya roki gwamnatin Najeriya ta tabbatar da bashi tsaro biyo bayan rahotonsa na jami'o'i masu bada digirin bogi.
Shirin 'Fulbright Teaching Execellence and Achievement Program' ya tahowa malamai yan Najeriya da dama na samun aikin koyarwa a Amurka bayan horaswa na sati shida.
Hukumar Kula da Jami'o'i na Najeriya (NUC) ta sanar da cewa ta fara bincike kan wasu jami'o'i 9 a kasar da ake zargin an kafa su ba bisa ka'ida ba.
Shugaban kungiyar NANS reshen jami'o'in Benin, Ugochukwu Favour ya nemi a kama dan jaridan da ya yi rahoton 'digiri dan Kwatano', inda ya ce barazana ne ga gwamnati.
Akwai dalibai 15, 000 da suke karatu a jami’o’in da aka tsaida karbar takardar shaidarsu a Benin. Kungiyar NANS ta roki gwamnatin Najeriya ta guji yin kudin goro.
Hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC), ta bayyana cewa ta kama wasu mutane da laifin gudanar da ayyukan haramtattun jami’o’i 37 a fadin kasar nan.
Karatun Ilimi
Samu kari