Hukuncin Wanda Maziyyi ko Maniyyi ya Fito Masa Alhali Yana Azumi a Watan Ramadan

Hukuncin Wanda Maziyyi ko Maniyyi ya Fito Masa Alhali Yana Azumi a Watan Ramadan

  • An yi wa Aminu Ibrahim Daurawa tambaya game da hukuncin zubar da maziyyi a cikin azumi a can shekarun baya
  • Babban malamin musulunci, Shiekh Aminu Ibrahim Daurawa ya ce wanda ya yi maziyyi zai rama azumi daya
  • Wannan shi ne ra’ayi da fatawar manyan malaman mazhabar Malikiyya irinsu Ibn Abi Zayd Al-Qayrawani
  • Sai dai wannan hukunci ya shafi wanda ya motsa sha'warsa ne da gangan ba wanda ya yi mafarki a barci ba

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Neman hukuncin maniyyi ko maziyyi da azumi

Wani Bawan Allah ya aiko wa Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa tambaya, inda ya nemi fatawa a kan zubar da maniyyi a lokacin da mutum yake azumi.

Wannan mutum ya bayyana cewa yana cikin yin waya da budurwarsa a wayar salula, sai ya ji maniyyi ya fito daga gabansa, alhali azumi yana bakinsa.

Kara karanta wannan

Fitaccen jarumi ya fadi yadda ya watsar da Musulunci da Kiristanci bayan dogon nazari

Maziyyi ko Maniyyi
Wata mace da wani rike da waya Hoto: Getty Images (An kawo hoton ne domin misali)
Asali: Getty Images

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Daurawa ya ja kunnen masu azumi

Kafin ya amsa tambayar, babban malamin na musulunci, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ja-kunne kan yin waya irin wannan a lokacin da ake azumi.

Shehin malamin ya ce ganganci ne mutum ya na dauke da azumi, ya rika yin wayar da za ta iya motsa masa sha’awa a cikin watan azumi na Ramadan.

Aminu Ibrahim Daurawa ya nakalto fatawar malamin fikihu nan, Ibn Abi Zayd Al-Qayrawani, wanda ya ce irin azumin wannan Bawan Allah ya karye.

Maziyyi da Maniyyi suna karya azumi

Sheikh Al-Qayrawani a littafinsa na Risala, ya ce wanda ya zubar da maziyyi da gangan a sanadiyyar sha’awa zai kama baki, sai ya rama azumi daya daga baya.

Haka zalika a fatawar bajimin malamin, duk wanda ya kai har ga zubar da maniyyi a lokacin azumi, sai ya yi kaffara; zai yi azumi 61 bayan watan na Ramadan.

Kara karanta wannan

Shahararren mawaki a Najeriya ya riga mu gidan gaskiya a yau Juma'a

Zakariyya El-Uthman ya wallafa bidiyon amsar tambayar nan a shafinsa na X. Da alamu an yi karatun ne a garin Gombe inda malamin ya saba tafsiri.

A kwanan baya an yi wa wani malami irin wannan tambaya, inda ya ba mai neman wannan amsa shawarar ya fara da yin aure domin ya magance sha’awarsa.

A wani kaulin da ya sha ban-bam da fatawar malaman mazhabar malikiyya, fitar maziyyi ba ya karya azumi, amma an hadu a kan hakan zai nakasa ladar mutum.

Goron azumi a watan Ramadan

A cikin irin wannan shirye-shirye na mu na goron Ramadan, kwanakin baya mun kawo maki jerin abubuwa 10 da ya kamata kowane Musulmi ya kiyaye da Azumi

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya yi magana game da abubuwan da ake bukatar mai azumi ya kiyaye. Daga ciki akwai karatun Kur'ani da kuma yawan yin salloli.

Asali: Legit.ng

Online view pixel