Gwamnatin Najeriya
Gwamnatin Kano ta nemi masu filaye da su gaggauta sabunta takardunsu. Kwamishinan kasa da tsare tsare, Abduljabbar Umar ya ce an sa wa'adin sabunta takardun.
Gwamnati ta aika N748,320 ga wata malama a jihar Katsina bisa kuskure. Kudin na daga cikin wanda ake amfani da shi don ciyar da dalibai, amma ta mayar da kudin.
Gwamnati ta ce 'yan Najeriya su fara sa rai da saukin rayuwa. Ministan yada labarai da wayar da kan jama'a, Mohammed Idris ne ya fadi haka a wani taro a Abuja.
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya taya Muhammadu Buhari murnar cika shekaru 82 a duniya inda ya yi masa fatan alheri a ranar zagayowar haihuwarsa.
Kamfanin rarraba wutar lantarki na kasa (TCN) ya kama wasu mutane shida da suka shahara da lalata turken wutar lantarki a Najeriya da jihar Ribas.
Rundunar tsaron Najeriya ta karyata jita jitar cewa sojojin Faransa sun shigo Maiduguri na jihar Borno domin kafa sansanin soji. Sojojin sun ce labarin karya ne.
Tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ya ba gwamnatin Bola Tinubu shawara kan zanga-zangar da aka yi. Ya ce ya kamata ta koma ta sake lale.
Ibrahim Mukhtar ba zai hakura da ruguza gininsa da jami’an KNUPDA suka yi a jihar Kano ba Yake cewa sun wayi gari ne kurum, sai suka ji labarin an kai ginin kasa.
Gwamnatin tarayya ta zargi Facebook da sabawa ka'idoji don haka aka ci ta tara. A yanzu alkali ya bukaci hukumar ARCON ta bar magaar wannan haraji na N60bn.
Gwamnatin Najeriya
Samu kari