Bayan Shafe Awa 24 a APC, Masoyin Pantami Ya Sake Komawa Gidan Malam
- Hon. Abubakar Sadiq Zakari ya koma tafiyar Pantamiyya da jam’iyyar PDP, bayan kwana daya sanar da ficewarsa
- Zakari ya ce ya sake nazarin matsayar siyasarsa ne bayan tuntuba da shawarwari daga ’yan’uwa, abokai da manyan mutane
- Ya nemi afuwar ’yan Pantamiyya da PDP, tare da jaddada cikakken goyon bayansa ga jagoransa, Farfesa Isa Ali Pantami
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Pantami, Gombe - Wani makusancin Farfesa Isa Ali Pantami ya koma gidan malam bayan sanar da ficewarsa daga tafiyar.
Hon. Abubakar Sadiq Zakari ya watsar da tafiyar gidan Malam inda ya yanke shawarar shiga jam'iyyar APC mai mulkin jihar.

Source: Facebook
Sai dai a wata sanarwa da ya wallafa a Facebook, Hon. Zakari ya bayyana dalilansa na dawo wa gidan malam da tafiyar PDP.
Dalilin dawowar Zakari gidan Pantami
A cikin sanarwar, matashin ya ce ya yanke shawarar ce bayan yin nazari da kuma tattaunawa da yan uwa da abokan arziki.
Ya nemi afuwar yan Pantamiyya da magoya bayanta da kuma PDP inda ya ce yana jaddada goyon bayansa ga Farfesa Isa Ali Pantami.
Sanarwar ta ce:
"Bayan zama, tuntuba da shawarwari daga manyan mutane masu dattaku, ’yan uwa da abokan arziki dangane da matsayar siyasar da na ɗauka ta ficewa daga Pantamiyya da kuma jam’iyyar PDP, ina mai sanar da jama’a cewa na sake yin nazari kan matakin da na ɗauka.
"Saboda haka, ina neman afuwar dukkan ’yan Pantamiyya Movement da magoya bayanta, tare da sanar da cewa na dawo cikin tafiyar Pantamiyya Movement da jam’iyyar PDP.
Ina kuma jaddada cikakken goyon bayana ga jagorana, Farfesa Isa Ali Pantami, tare da ci gaba da girmama shi da kuma dukkan ’yan tafiyar."

Source: Twitter
Afuwar da Zakari ya nema a siyasance
Hon Zakari ya kuma nemi afuwa bisa abin da ya faru kan lamarin, musamman ganin yadda lamarin ya jefa wasu daga cikin ’yan tafiyar da masoyanta cikin damuwa da jimami.
Ya ce ya samu kiraye-kiraye da shawarwari masu yawa daga ’yan’uwa, abokai da masoya, waɗanda suka nemi ya sake duba matsayar da ya ɗauka.
Matashin ya kuma yi wa mutanen jam'iyyar APC da na yi kwana daya a cikinsu fatan alheri bisa yadda suka tarbe shi inda ya bayyana godiya sosai da karimchi.
Ya kara da cewa:
"Ina mai tabbatar wa da kowa cewa wannan mataki na komawa cikin tafiyar an ɗauke shi ne cikin fahimta, mutunci da kuma kishin makomar siyasa ba don son rai ba."
Tsohon sanata ya dawo tafiyar Pantami
Mun ba ku labarin cewa tsohon Sanatan Gombe ta Arewa, Ambasada Haruna Garba, ya bayyana goyon bayansa ga Farfesa Isa Ali Pantami, tare da mika masa cikakken tsarin siyasar sa.
Haruna Garba ya umarci magoya bayansa da su mara wa Pantami baya tare da hada kai da shi domin zaben 2027 da kuma bayan haka.
Sanatan ya ce ayyukan Pantami a mukaman da ya taba rike wa, da kuma kwarewarsa a harkokin cikin gida da na kasa da kasa, ne suka sa ya goyi bayansa.
Asali: Legit.ng


