Ba Za a Yi Haka Ba: Kungiya Ta Yi Martani kan Kiran a Kori Shugaban NSCDC kan Mutuwar Matasa a Neja
- Kungiyar COCSTA ta yi watsi da kiran a kori shugaban NSCDC Ahmed Abubakar Audi kan mutuwar mutane 37 da ake zargi da hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba a Minna
- Kungiyar ta ce Kwamandan NSCDC na jihar Neja ya amince cewa bai sanar da Audi game da kamen ba kafin mutuwar wadanda ake zargin
- Gwamnatin Tarayya ta dakatar da kwamandan jihar Neja tare da kafa kwamitin mutum 10 domin gudanar da bincike kan lamarin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Minna, jihar Neja — Wata kungiyar farar hula ta yi watsi da kiran a kori Shugaban Hukumar Tsaron Fararen Hula ta Najeriya (NSCDC), Farfesa Ahmed Abubakar Audi, kan mutuwar mutane 37 da ake zargi da hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba a Minna, jihar Neja.
Kungiyar Coalition of Civil Societies for Transparency and Accountability (COCSTA) ta bayyana kiran da wani lauya kuma mai rajin kare hakkin bil'adama, Hamza N. Dantani, ya yi da cewa bai dace ba kuma yana iya karkatar da hankali daga ainihin batun.
A cikin wata sanarwa da Mai Gudanar da Kungiyar na Kasa, Comrade Bilal Galadima, ya sanya wa hannu a ranar 20 ga Satumba 2026, COCSTA ta ce ya kamata a bar binciken da ake gudanarwa ya kammala kafin yanke hukunci.

Source: Twitter
Yadda mutanen suka mutu
A cewar NSCDC, jami'anta sun kama mutane sama da 50 da ake zargi da hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba yayin wani samame da aka gudanar a ranar 15 da 16 ga Satumba 2026 a yankin gidajen Lt. Gen. Mohammed Inuwa Wushishi Housing Estate da ke Minna.
Mai magana da yawun hukumar, Babawale Afolabi, ya ce ba a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu ba, domin jami'an na ci gaba da tantance bayanansu da yin sauran takardun da suka dace lokacin da mutuwar ta faru.
COCSTA ta ce Kwamandan NSCDC na jihar Neja, Suberu Siyaka Aniviye, ya amince cewa bai sanar da Audi game da kama mutanen ba kafin faruwar lamarin.
Kungiyar ta ce saboda haka, bai kamata a dora wa kwamanda janar alhakin abin da ta kira gazawar aiki a matakin kwamandan jihar ba, musamman ganin cewa an tsallake tsarin bayar da rahoto na hukumar.
Gwamnati ta dakatar da kwamanda
Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Aniviye tare da kafa kwamitin mutum 10 mai zaman kansa domin binciken musabbabin mutuwar mutanen.
COCSTA ta bukaci dukkan bangarorin da su bar binciken da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Ministan Harkokin Cikin Gida, Dr Olubunmi Tunji-Ojo, suka bayar da umarnin gudanarwa ya kammala.
Kungiyar ta kuma tambayi Dantani dalilin da ya sa bai nemi a kori shugabannin hukumomin tsaro ba bayan wasu hare-haren soji da suka yi sanadin mutuwar fararen hula 85 a wani taron addini a Tudun Biri, Kaduna.
Ta kuma ambaci wasu makamantan abubuwan da suka faru a jihohin Zamfara, Sokoto da Borno, : kuma kisan da ya faru yayin zanga-zangar #EndSARS.
Galadima ya ce duk wanda bincike ya tabbatar da cewa yana da hannu a lamarin ya kamata ya fuskanci hukuncin da ya dace da doka.
Ya ce COCSTA na ganin ya kamata a bar tsarin shari'a da bincike ya bi hanyarsa, maimakon yanke hukunci tun kafin kammala binciken.
Asali: Legit.ng

