Dalilin Atiku na Jawo Amaechi Su Yi Takarar Shugaban Kasa tare a ADC Ya Fito Fili
- Kenneth Okonkwo ya nuna abin da ya sa Rotimi Amaechi ya samu tikitin takara a jam’iyyarsu ta ADC
- Atiku Abubakar ya tafi da tsohon gwamnan Rivers ne ganin kusan ya fi kowa kusanci da ‘yan kabilar Ibo
- Sauya-shekar Peter Obi zuwa NDC ta kawo wa Atiku cikas, Mista Okonkwo ya ce shiyasa aka tafi da Amaaechi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada
Abuja - Babban kusa a jam’iyyar ADC, Kenneth Okonkwo, ya kare matakin da Atiku Abubakar ya dauka na jawo Rotimi Amaechi.
Atiku Abubakar ya zabi Rotimi Amaechi ya zama abokin gaminsa, ya zama masa ‘dan takarar mataimakin shugaban kasa na ADC.

Source: Getty Images
Keneth Okokwo ya yi maganar tikitin ADC
An ji Keneth Okonkwo a tashar Channels ya ce an jawo shi ne domin ka da mutanen Kudu maso gabas su ji ana yi babu su a jam’iyyar.
Da aka yi masa magana game da zabin tsohon ministan sufurin, sai ‘dan siyasar ya yi bayanin yadda ADC ta iya cin ma wannan matsaya.
Wasu sun so abokin gamin Atiku Abubakar ya zama Ibo daga Kudu maso gabas kamar yadda ‘dan siyasar ya saba yi a zabukan baya.
Mista Okonkwo ya ce sai da ta yi zama na cikin gida, aka tuntubi manyan ‘ya ‘ya kuma aka shawo kan duk wasu korafi da za a samu.
A hirar ya ce daukacin ‘yan jam’iyyar hamayyar suna goyon bayan tikin Atiku-Amaechi. The Sun ta dauko rahoton a ranar Alhamis.
Kenneth Okonkwo ya ce:
“ADC ta sanar da Rotimi Amaechi a matsayin ‘dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar
Kuma yadda mu ke aikinmu, idan irin hakan ta tashi…mukan zauna a bayan labule mu sasanta, a tattauna a siyasance domin a samuy matsaya, kuma mu hada kai mu yi aiki.
Kakakin yakin neman zaben na Atiku ya ce ana faman tattauna wa a yanzu domin shawo kan korafe-korafe kuma a shiryawa zaben 2027.

Kara karanta wannan
Yadda ‘yan sanda suka shiga suka fita aka damko shugaban ma’aikatar bogi a wani kauye
Tsohon ‘dan wasan kwaikwayon ya gyara maganganun da ya yi a baya, ya ce tun farko shi bai adawa da Rotimi Amaechi a jam’iyyarsu ta ADC.
Abin da Okonkwo yake nema shi ne a samu Ibo a tikitin shugaban kasa ganin ba su taba shiga Aso Rock ba tun daga shekarar 1999 har zuwa yau.

Source: Getty Images
A cewarsa, ficewar Peter Obi daga ADC ta lahanta Atiku Abubakar, sai ya bar shi bai da zabi sosai daga jihohin da ke Kudu maso gabas.
Saboda babu yadda zai yi, Okonkwo ya ce sai Atiku ya zakulo Amaechi domin yana da kusanci na siyasa da yanki da mutanen kabilar Ibo.
Tsohon ‘dan wasan kwaikwayon ya kuma ce Atiku bai da wata kiyayya a kan Ibo kuma yanzu duk kansu a hade yake kuma babu baraka.
Shiyasa duk da haka Atiku Abubakar ya tafi ya dauko mutumin da ya fi kusanci da Kudu maso gabas.
- Kenneth Okonkwo
Peter Obi zai ci zabe a 2027?
Rahoto ya zo cewa Sanatan Kano, Rufai Hanga ya sace guiwar Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi hasashen Atiku Abubakar zai sha gaban Peter Obi
Sanatan wanda na hannun daman Kwankwaso ne ya ce Peter Obi ba zai ci zabe a 2027 ba, amma yana ganin ADC za ta iya ganin bayan APC.
Rufai Hanga, ya ce 'dan takaran ADC a Anambra kurum zai ci zabe kuma Kwankwaso Kano kurum yake da karfi, a nan ma rabi-da-rabi a halin yanzu.
Asali: Legit.ng

