An Kashe Bakin Tsanya, Kudan da aka 'Nadi Muryarsa' Ya Gana da El Rufa'i da ke Hannun ICPC
- Ana tsaka da maganganu kan wni sautinmurya da aka nada na Isa Ashiru Kudan game da Nasir El-Rufa'i, an hango 'dan takarar gwamnan a ICPC
- An rika cece-kuce a kan zargin Kudan ya yi wa Nasir El-Rufa'i tas a wani sautin murya, inda ya ce yana tare da tsohon gwamnan saboda tikitin takara
- Amma dan takarar gwamnan na ADC ya ce ganawar ta kara masu kwarin gwiwar tunkarar zaben 2027 a Kaduna duk da kotu ta hana balin El-Rufa'i
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Kaduna - Dan takarar gwamna na jam'iyyar ADC a jihar Kaduna, Isa Ashiru Kudan, ya gana da tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir Ahmed El-Rufai.
Tattaunawarsu ta zo a daidai lokacin da ake ta ce-e-kuce game da wani sautin murya da aka ce yana da alaka da shi, inda ya caccaki tsohon Kudan ya soki tsohon gwamnan.

Source: Facebook
Jaridar Daily Trust ta wallafa da cewa Kudan ya tabbatar da cewa ya gana da El-Rufai, sai dai bai bayyana inda aka gudanar da ganawar ba.
Kudan ya gana da El-Rufa'i
Trust TV ta kawo labarin cewa sanawar ta zo ne bayan wani sautin murya da aka yada a kafafen sada zumunta, wanda aka ce na dan takarar gwamnan ADC ne, ya haddasa muhawara a cikin jam'iyyar.
Sai dai magoya bayan Isa Ashiru Kudan sun yi watsi da sautin, suna mai cewa an kirkire shi ne domin bata masa suna. Haka kuma magoya bayan El-Rufai sun sake jaddada goyon bayansu ga tsohon gwamnan duk da wannan cece-kuce.
A wani bangare kuma, Aisha El-Rufai, matar tsohon gwamnan Kaduna, ta fito fili ta bayyana cewa tana goyon bayan takarar Isa Ashiru a karkashin jam'iyyar ADC.
ADC ta shirya kifar da APC - Kudan
Da yake karin haske kan ganawar, Isa Ashiru ya ce tattaunawar da suka yi da Nasir El-Rufai ta kara masu kwarin gwiwa da hadin kai yayin da suke shirin fuskantar zaben gwamnan jihar Kaduna na shekarar 2027.

Source: Facebook
Ya bayyana cewa jam'iyyar ADC ta shirya tsaf domin kalubalantar gwamnatin APC a jihar, wacce ya zarga da gaza cika alkawuran da ta daukar wa al'ummar Kaduna.
A cewarsa, ganawar ta tabbatar masu cewa lokaci ya yi da za a hada kai domin dawo da adalci, ci gaba da mutuncin al'umma a jihar.
Isa Ashiru Kudan ya ce ADC ba wai kawai ta shirya shiga zabe ba ne, har ma tana da karfin da za ta kayar da gwamnatin APC a Kaduna.
Ya kuma yi zargin cewa gwamnatin mai ci ta gaza magance matsalolin da suka addabi jama'a, yana mai cewa al'ummar jihar sun gaji da wahalhalu da kuma uzurorin da ake bayarwa.
A halin yanzu dai, Nasir El-Rufai na ci gaba da kasancewa a tsare a hannun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa Mai Zaman Kanta (ICPC) bisa zargin aikata rashawa a lokacin da yake gwamnan jihar Kaduna.
An nadi 'muryar' Kudan kan El-Rufa'i
A baya, mun kawo labarin ana zargin an nadi muryar Isa Ashiru Kudan yana wasu maganganu marasa dadi a wayar salula game da Nasir El-Rufai, inda magoya bayan ‘dan takarar gwamnan sun ce babu mamaki aikin makiya.
Magoya bayan sun bayyana cewa sun yi amfani da fasahar AI wajen kirkirar sautin. Amma a gefe guda matar Nasir El-Rufai ta shaida wa al’umma a jihar Kaduna cewa Isa Kudan za su mara wa baya a zaben gwamna mai zuwa.
Amma wani jagora a ADC kuma mutumin Isa Ashiru Kudan ya karyata zargin, ya ce sautin da ake yawo da shin a bogi ne da wasu suka kirkira tare da neman jama'a su yi watsi da duk irin wadannan maganganu.
Asali: Legit.ng


