Kaduna: Ana Zargin An Nadi Muryar Isa Ashiru Yana Caccakar El Rufai a Wayar Tarho
- Ana zargin an nadi muryar Isa Ashiru Kudan yana wasu maganganu marasa dadi a wayar salula game da Nasir El-Rufai
- Magoya bayan ‘dan takarar gwamnan sun ce babu mamaki makiya ne suka yi amfani da fasahar AI wajen kirkirar sautin
- Wata matar Nasir El-Rufai ta shaida wa al’umma a jihar Kaduna cewa Isa Kudan za su mara wa baya a zaben gwamna
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M. Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada
Kaduna - An nadi wani sauti da ake zargin an ji ‘dan takaran PDP a zaben gwamnan jihar Kaduna, Isa Ashiru Kudan yana wasu maganganu.
Ana zargin cewa sautin ya nuna Hon. Isah Ashiru Kudan yana yin wasu maganganu da mutanen Nasir El-Rufai sam ba za su ji dadinsu ba.

Source: Getty Images
Isa Ashiru: Iyalan El-Rufai sun ji sun gani
Amma duk da haka, jaridar Daily Trust ta rahoto cewa mai dakin tsohon gwamnan, Aisha El-Rufai ta nuna suna nan tare da ‘dan takaran na ADC.
Aisha El-Rufai wanda tana cikin matan tsohon gwamnan na Kaduna ta yi amfani da shafinta na Facebook tana nuna wanda take goyon baya.
“Babu gudu, babu ja da baya. Shure-shure bai hana mutuwa.”
Aisha El-Rufai ta ce ko Isa Ashiru Kudan zai casa duka iyalin El-Rufai ne ba shi tsohon gwamnan kadai, ba su goyon bayan tazarcen mulkin APC.
Sakon nata ya nuna ba za su mara wa Uba Sani baya a zaben 2027 duk da ana zargin ‘dan takaran ADC bai tare da El-Rufai tsakani da Allah.
Sautin Isa Ashiru da ake zargin ya fita
A faifen da Legit Hausa ta saurara, ana zargin cewa Isa Kudan ya fada wa wani a wayar tarho cewa saboda ya samu tikiti ne kawai ya shiga ADC.
Idan da gaske muryar shi ce, ‘dan siyasar ya kuma caccaki El-Rufai, yana nesanta kan shi da tsohon gwamnan da yake cewa ya zalunce shi a baya.
‘Dan takaran har ya kara da cewa zaluncin da Malam El-Rufai ya yi a baya ne yake bin shi, a karshe yanzu ya shafe kwana da kwanaki yana tsare.

Source: Facebook
'Yan APC suna tare da Isa Ashiru Kudan
Amma wani jagora a ADC kuma mutumin Isa Ashiru Kudan ya karyata zargin, ya ce sautin da ake yawo da shin a bogi ne da wasu suka kirkira.
Duk da ya ce bai da hurumin magana, ‘dan siysar ya ce an kirkire shi ne da nufin a bata gwaninsu.
A matsayinsu na ‘ya ‘yan jam’iyya, ya bayyana cewa sun yi zama kuma aka tabbatar da cewa kowa a ADC yana tare da ‘dan takaran gwamnan.
Sannan kuma za a sake yin wani zama da nufin a tabbatar da matsayar mutanen El-Rufai, amma dai har yanzu Isa Ashiru bai ce uffan ba tukuna.
Kwankwaso zai hade da Ganduje a NDC?
Ana kishin kishin din hadewar Abdullahi Umar Ganduje da Rabiu Musa Kwankwaso a NDC har da samun takarar Sanatan yankin Kano ta Arewa.
Tun da Dr. Abdullahi Umar Ganduje OFR ya zama gwamna a Kano, aka samu sabani tsakaninsa da magabancin nasa wanda suke tare tun a 1999.
Tsohon kwamishina ya tanka rade-radin haduwar Kwankwaso da Ganduje, yake cewa idan ta tabbata, to karshen tsohon mai gidansa sa ne ya zo.
Asali: Legit.ng

