Tsohon Minista daga Arewa Ya Rasu, Gwamnonin yankin Sun Tuna Alherinsa

Tsohon Minista daga Arewa Ya Rasu, Gwamnonin yankin Sun Tuna Alherinsa

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya ta yi alhinin rasuwar tsohon Ministan Kudi a kasar, Alhaji Abubakar Alhaji
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya ce marigayin ya taka muhimmiyar rawa a Ma'aikatar Tsare-tsaren Kasa, Ma'aikatar Kudi da kuma sauran mukamai
  • Gwamnonin Arewa sun miƙa ta'aziyya ga iyalansa, Sarkin Musulmi, gwamnatin Sokoto da daukacin 'yan Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Gombe - Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya (NNGF) ta yi martani game da rashin da aka yi na tsohon minista a Najeriya.

Kungiyar ta bayyana alhini kan rasuwar tsohon Ministan Kudi kuma Sardaunan Sokoto, Alhaji Abubakar Alhaji, wanda ya rasu ranar Alhamis a Abuja.

Tsohon minista ya rasu a Najeriya
Tsohon babban kwamishinan Najeriya a Birtaniya, Alhaji Abubakar Alhaji Hoto: Almustapha Jadadi.
Source: Facebook

Hakan na cikin sakon ta'aziyya da sakataren shugaban kungiyar, Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana a Facebook.

Sardaunar Sokoto: Gwamnonin Arewa sun yi jimami

Kara karanta wannan

'Kuskuren da Atiku, Obi da Kwankwaso ke yi da zai ba Tinubu mulki a sauƙi'

Sanarwar ta tabbatar da marigayin a matsayin fitaccen jami'in gwamnati kuma dattijo mai kishin kasa wanda ya ba da gudunmawa sosai.

Ya tuna cewa Alhaji Abubakar Alhaji ya yi aiki a matsayin Ministan Tsare-tsaren Kasa kafin daga baya ya zama Ministan Kudi a gwamnatin Janar Ibrahim Babangida.

Gwamnan ya ce marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen tsara manufofin tattalin arzikin Najeriya, inda ya ba da gudummawa mai yawa ga ci gaban kasa.

Ya kuma bayyana cewa bayan kammala aikinsa na minista, an naɗa shi Babban Kwamishinan Najeriya a Birtaniya a shekarar 1992, inda ya ci gaba da yi wa kasa hidima.

Inuwa Yahaya ya kuma yaba wa marigayin saboda asalinsa na zuri'ar Shehu Usmanu Danfodiyo, yana mai cewa ya kasance mai kare tarihi da al'adun Daular Usmaniyya ta Sakkwato.

Sanarwar ta ce:

"A madadin gwamnonin jihohin Arewa 19, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya miƙa ta'aziyyarsa ga iyalan marigayin, da Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar na III, da daukacin Masarautar Sokoto, da gwamnati da al’ummar Sokoto, tare da dukkan ’yan Najeriya da ke jimamin rasuwar wannan fitaccen dattijin ƙasa."

Kara karanta wannan

Sardaunan Sokoto, Abubakar Alhaji ya riga mu gidan gaskiya

Gwamna Inuwa ya yi jimamin mutuwar tsohon minista
Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe, kuma shugaban gwamnonin Arewa. Hoto: Ismaila Uba Misilli.
Source: Facebook

Ta'aziyyar gwamnonin Arewa ga iyalan tsohon minista

Gwamnan ya ce rasuwar Alhaji Abubakar Alhaji babban rashi ne ga iyalansa, al'ummar Sokoto, Arewacin Najeriya da kuma kasa baki ɗaya saboda kwarewarsa da nagartaccen shugabanci.

A madadin gwamnonin jihohin Arewa 19, Gwamna Inuwa Yahaya ya miƙa ta'aziyya ga iyalan marigayin, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Sa'ad Abubakar na Uku da Daular Usmaniyya.

Haka kuma ya jajanta wa gwamnatin da al'ummar Sokoto tare da dukkan 'yan Najeriya da ke alhinin rasuwar wannan fitaccen dattijo mai hidimar kasa.

Sakon ya ƙare da addu'ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa Alhaji Abubakar Alhaji kura-kuransa, Ya saka masa da Aljannar Firdausi bisa rayuwar hidimar da ya yi wa Najeriya.

Tsohon babban alkali ya rasu a Borno

Mun ba ku labarin cewa an shiga jimami bayan sanar da rasuwar tsohon alkalin Babbar Kotun Tarayya daga jihar Borno da ke Arewacin Najeriya.

Mai shari'a Babagana Ashigar, ya rasu a Maiduguri bayan gajeruwar rashin lafiya, lamarin da ya jawo alhini tsakanin ma'aikatan shari'a da iyalansa.

An yi jana'izarsa ranar Asabar bisa koyarwar addinin Musulunci, yayin da Babbar Kotun Tarayya ta bayyana cewa ya yi aiki da gaskiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.