Babbar Magana: Gwamnatin Tinubu za Ta Zare Tallafin Lantarki a 2027
- Gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu tana shirin cire tallafin bangaren wutar lantarki a hankali inda za a fara daga shekarar 2027
- Game da karin kudin wuta, ministan ya ce ba za a sami karin kudin wuta ba nan take ga masu amfani da wutar lantarki a yau da kullum
- Ya ce za a cire tallafin ne daki-daki domin tabbatar da cewa ba a hana al'umma amfanin da suke samu ba, tare da daidaita bashin da ake bi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ta sanar da tsarin janye biyan tallafi a bangaren wutar lantarki da za a fara daga shekarar 2027.
Ministan makamashi, Joseph Tegbe, ne ya bayyana wannan tsari a lokacin wani taro da manema labarai a ranar Juma'a, yayin da yake magana kan bashi da ake babi a bangaren wutar lantarkin.

Source: Facebook
The Cable ta wallafa cewa ya ce za a cire tallafin ne a hankali, amma ya tabbatar da cewa 'yan Najeriya ba za su shiga babbar matsala ba.
Haka zalika, ministan ya sake jaddada cewa babu wani shiri na kara kudin wutar lantarki nan take bayan zare tallafin.
Karin bayani na tafe...
Asali: Legit.ng
