Tafiyar Atiku Ta Shiga Matsala a Gombe, 'Yan ADC Sun Koma APC da PDP
- 'Yan jam'iyyar ADC a jihar Gombe na sauya sheka zuwa jam'iyyun APC, PDP da sauransu tun bayan zaben fitar da gwani da aka yi
- Sakataren jam'iyyar ADC a jihar Gombe, Dr Ahmad Gana ya sauya sheka zuwa APC, inda ya samu tarba ta hannun Jamilu Gwamna
- Wasu 'yan siyasa da suka nemi takara a karkashin jam'iyyar ADC, Dr Muhammad Bello da Mubarak Musa Dantori sun sauya sheka
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Gombe - Jam'iyyar ADC na fuskantar rudani a jihar Gombe bayan zaben fitar da gwani da ta gudanar a watan da ya gabata.
Wasu 'yan jam'iyyar ADC, ciki har da manyan shugabanni na sauya sheka zuwa PDP da APC domin samun mafakar siyasa.

Source: Facebook
Sakataren ADC ya koma jam'iyyar APC
Hadimin dan takarar gwamnan Gombe a karkashin APC, Ibrahim Sani Shawai ya wallafa a Facebook cewa sakataren ADC, Dr Ahmad Gana ya koma APC.
Ya ce:
"Dr Gana, ƙwararren jami’in gwamnati kuma tsohon kwamishina, ya miƙa takardar murabus daga mukaminsa a ADC, yana mai cewa ya gamsu cewa Dr Gwamna ne ya fi cancanta ya jagoranci jihar Gombe a wannan muhimmin lokaci."
Tun a ranar 20 ga watan Mayun 2026 Dr Ahmad Gana ya yi rubutu a shafinsa na Facebook yana ba APC shawara kan yadda za ta magance rikicin da ya bulla bayan hana Sheikh Pantami da Saidu Alkali takarar gwamna.
Lamarin ya jawo zarge-zarge daga masu magana a sashen sharhi, suna cewa dama yana yi wa APC aiki ne. Ga sakon da Dr Gana ya rubuta a lokacin:
"Ga maslaha ga makwabtan mu na siyasa. Shi minista (Saidu Alkali) a maida shi kujerar sa, shi kuma akaramakallah (Pantami) a tura shi ambasada. Shikenan"

Source: Facebook
'Dan takarar ADC ya koma APC
Tsohon dan majalisar jihar Gombe, Muhammad A Bello da ya nemi takarar majalisar tarayya a ADC a mazabar Gombe/Kwami/Funakaye, ya koma APC.
Ya bayyana haka ne bayan gaza samun tikitin takara a zaben fitar da gwani da aka yi, inda ya yi zargin ba a yi masa adalci ba.
Mai magana da yawun gwamnan jihar Gombe, Ismaila Uba Misilli, ya wallafa a Facebook cewa Dr Bello zai yi wa APC aiki a jihar.

Source: Facebook
Dantori ya koma jam'iyyar PDP
Mubarak Musa Dantori da ya nemi takarar majalisar jihar a Gombe ta Kudu karkashin jam'iyyar ADC ya sanar da komawa PDP bayan gaza samun tikiti.
A wani sako da ya wallafa a Facebook, Dantori ya ce:
"Bayan tattaunawa mai zurfi, nazari mai kyau, da kuma shawarwari masu amfani daga magoya bayana, abokan siyasa da dattawa masu daraja, na yanke shawarar komawa jam’iyyar PDP."

Source: Facebook
Dantori ya ce ya yanke shawarar ba da cikakken goyon baya ga Sheikh Isa Ali Ibrahim Pantami domin ya zama gwamna a ƙarƙashin tutar PDP a jihar Gombe.
Tinka ya samu tikitin ADC a Gombe
A wani labarin, mun kawo muku cewa jam'iyyar ADC ta sanar da cewa Dr Bala Bello Tinka ne ya lashe zaben fitar da gwani da ta yi a Gombe.
A bayanin da jam'iyyar ta yi, ta ce dukkan masu ruwa da tsaki sun amince da Dr Bala Bello Tinka ya yi takarar gwamna a jihar a zaben 2027.
A jawabin karbar tikitin da ya yi, dan takarar ya ce a shirye ya ke ya yi ayyukan cigaba a jihar Gombe matukar aka kada masa kuri'a ya zama gwamna.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


