Rikicin ADC: Kotu Za Ta Yi Zama kan Shari'ar Nafiu Bala da Tsagin David Mark
- Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsayar da ranar Juma’a, 8 ga watan Mayu, domin ci gaba da shari’ar rikicin shugabancin jam’iyyar ADC
- Wannan ya biyo bayan hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke a karar da David Mark ya shigar, inda aka umarci babbar kotun ta ci gaba da saurari shari'ar
- Rikicin ya fara ne bayan Nafiu Bala Gombe ya shigar da ƙara, yana ƙalubalantar David Mark da Rauf Aregbesola a matsayin shugabannin ADC
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta sa ranar Juma'a, 8 ga watan Mayu, domin sauraron shari'ar rikicin shugabancin jam'iyyar ADC tsakanin Nafiu-Bala Gombe da tsagin Sanata David Mark.
A ranar Laraba ne aka tattaro ccewa an riga an aika wa ɓangarorin da abin ya shafa takardar gayyata domin su bayyana a gaban mai shari'a, Justice Emeka Nwite.
ADC: Za a saurari shari'ar Nafiu Bala
Justice Nwite ya tsayar da wannan rana ne biyo bayan wata wasiƙar neman ranar sauraron ƙara mai lamba FHC/ABJ/1819/2025, wadda lauyan mai ƙara, Luka Haruna (SAN), ya shigar, in ji rahoton Daily Trust.
Wasiƙar, wadda aka rubuta aka kuma shigar a ranar 5 ga Mayu, ta bayyana cewa:
“Biyo bayan hukuncin da Kotun Koli ta yanke a ranar 30 ga Afrilun 2026 kan ƙarar da Sanata David Mark ya shigar, muna neman a ba mu rana domin gaggauta sauraron wannan magana daidai da hukuncin kotun daukaka kara.
"A tare da wannan takarda, akwai kwafin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, wacce ta bukaci a gaggauta sauraro da yanke hukunci a wannan shari'ar."
A ranar 14 ga Afrilu, 2026, Mai shari'a Nwite ya ɗage sauraron shari'ar har sai abin da hali ya yi, biyo bayan buƙatar Nafiu Gombe na jiran hukuncin Kotun Ƙoli kan karar da Mark ya shigar.
Shari'ar rikicin shugabancin jam'iyyar ADC
Nafiu Bala Gombe, wanda tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar ADC ne na ƙasa, ya shigar da ƙarar ne domin neman kotu ta hana David Mark (Shugaban Jam’iyya) da Ogbeni Rauf Aregbesola (Sakataren Jam’iyya) ci gaba da bayyana kansu a matsayin shugabannin jam’iyyar.
Ya shaida wa kotu cewa bayyanar Mark da Aregbesola a matsayin shugabannin jam’iyyar ya saɓa wa tanadin kundin tsarin mulkin jam’iyyar da kuma Dokar Zaɓe ta ƙasa.
Sai dai, David Mark, wanda ake kara na biyu a shari'ar da Nafiu ya shigar a babbar kotun tarayya, ya kai maganar zuwa Kotun Koli don kalubalantar hukuncin kotun daukaka kara na ranar 12 ga Maris.
Bukatar Nafiu Gombe kan shari'ar ADC
A cikin ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/1819/2025, Nafiu Gombe ya shigar da ƙarar jam'iyyar ADC, David Mark, Rauf Aregbesola, Hukumar Zaɓe ta INEC, da kuma Ralph Nwosu.
Babban burin Nafiu Bala Gombe shi ne kotu ta tabbatar da cewa, an bi haramtacciyar hanya wajen nada shugabancin su David Mark, sannan kotu ta hana wadanda ake kara gudanar da taro ko jagorantar ayyuka da sunan ADC
Asali: Legit.ng

