Matar da APC Ta Tsaida Takara a Katsina Ta Fara Fuskantar Cikas daga Malaman Musulunci

Matar da APC Ta Tsaida Takara a Katsina Ta Fara Fuskantar Cikas daga Malaman Musulunci

  • Malaman addinin musulunci sun yi fatali da matakin tsaida mace a matsayin 'yar takarar kujerar Majalisar wakilai a mazabar Mani da Bindawa
  • Sun bayyana cewa musulunci ya hani al'umma dora mata a matsayin shugabanni, inda suka yi kira ga jama'a da kar su zabe ta
  • Sai dai kwamandan Hisbah na Katsina, Sheikh Abu Ammar yana da fahimtar da ta saba wa wannan kan batun shugabancin mata

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina – Wasu malaman addinin Musulunci a kananan hukumomin Mani da Bindawa na jihar Katsina sun bukaci al’umma da kada su zabi Jamila Abdu-Mani, ‘yar takarar APC a zaben majalisar wakilai na 2027.

Hajiya Jamila, wacce ta rike mukamin mai ba gwamna shawara kan ilimin ‘ya’ya mata, ta samu tikitin jam’iyyar APC ne ta hanyar tsarin sulhu, inda ta doke dan majalisa mai ci, Hon. Ahmad Yusuf, da sauran masu neman takara.

Kara karanta wannan

2027: APC ta kwantar da hankalin Pantami, ta ba shi dama kan batun takarar gwamna a Gombe

Jamila Abdu Mani.
Yar takarar APC a mazabar dan Majalisar tarayya na Mani da Bindawa, Katsina, Hajiya Jamila Abdu Mani Hoto: Tijjani I. Jibrin
Source: Facebook

Malamai sun nuna rashin amincewa

Premium Times ta ce wani malami mai suna, Malam Abu Abdullahi ya bayyana rashin jin dadinsa, yana mai cewa bai dace a ba mace shugabanci ba bisa koyarwar hadisai.

Ya ce:

“Manzon Allah (SWA) ya gargade mu game da bai wa mata shugabanci. Me ya sa za mu kauce wa koyarwar addinin mu?”

Haka kuma wani malami a Bindawa, Usman Salisu, ya bukaci shugabannin yankin da su kalubalanci matakin zaben ‘yar takarar jam'iyya mai mulki, yana mai cewa hakan ya saba da ka’idojin Musulunci.

Abu Ammar ya saba wa fahimtarsu

Sai dai kwamandan rundunar Hisbah na jihar Katsina, Abu Ammar, ya taba bayyana cewa Musulunci bai hana mata rike mukaman shugabanci ba, matukar ya dace da dabi’u da al’adun al’umma.

Malamim musuluncin ya ce mata na da damar rike mukamai idan hakan bai saba da ka’idojin zamantakewa da tarbiyya ba.

Kara karanta wannan

Atiku da shugabannin ADC sun fara shirin bin Kwankwaso zuwa NDC? Gaskiya ta fito

Tarihin mata a siyasar Katsina

Duk da cewa mata sun taba rike mukaman gwamnati a jihar Katsina, samun nasara a zabuka ya kasance kalubale saboda rashin yawan tsayar da su takara daga manyan jam’iyyu.

Malam Dikko Radda.
Gwamnan Katsina, Malam Dikko Radda yayin ganawa da tawagar magoya bayansa na Gwagware Support Group a fadar gwamnatinsa Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

A shekarar 1991, Mariya Abdullahi ta taba lashe zaben majalisar wakilai a yankin Bakori/Danja, yayin da Hadiza Bala Usman ta tsaya takara a 2011 amma ba ta yi nasara ba.

Hadiza Bala Usman ta tsaya a CPC domin wakiltar mutanen Musawa da Matazu a Majalisar tarayya.

Haka kuma, wasu kananan hukumomi kamar Mani, Bakori, Dutsin-Ma da Kurfi sun taba samun shugabanni mata a lokuta daban-daban, kamar yadda Daily Post ta kawo.

APC ta bai wa 'dan Mangal takarar Majalisa

Awani labarin, kun ji cewa Hon. Sani Aliyu Danlami, mai wakiltar Katsina ta tsakiya a Majalisar wakilai ya rasa tikitin neman takara karo na uku a zaben 2027.

Danlami, wanda ke wa’adinsa na biyu a majalisar wakilai, ya sha kaye ne bayan tattaunawa mai zafi da aka shafe kwanaki ana yi tsakanin manyan jiga-jigan APC da kwamitin sulhu na mazabarsa.

Kwamitin sulhu da Gwamna Dikko Radda ya kafa, ya amince da Abba Mangal, daya daga cikin ’ya’yan fitaccen attajiri, Dahiru Mangal, a matsayin dan takarar APC a mazabar Katsina ta Tsakiya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262