Rikici na Neman Barkewa a ADC, 'Yan Kwankwasiyya Sun Yi Wa Atiku Tatas kan Kwankwaso

Rikici na Neman Barkewa a ADC, 'Yan Kwankwasiyya Sun Yi Wa Atiku Tatas kan Kwankwaso

  • 'Yan Kwankwasiyya sun maida martani ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar kan kalaman da ya yi game da Kwankwaso
  • Kungiyar ta bayyana cewa Kwankwaso da Peter Obi ne kadai mutane ke goyon bayansu tsakani da Allah, ba don kudi ko tilasci ba
  • Kwankwasiyya ta kuma yi fatali da ikirarin Atiku cewa farin jinin Kwankwaso a Kano ya ragu, tana mai cewa hakan ba gaskiya ba ne

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Kungiyar Kwankwasiyya ta yi watsi da kalaman tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da ke nuna cewa tasirin siyasar Rabiu Musa Kwankwaso a Kano ya ja baya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake tsere da fafutukar neman tikitin takarar shugaban kasa a karkashin hadakar jam’iyyun adawa ta ADC.

Kara karanta wannan

Zaben 2027: "Kwankwaso ya amince ya zama abokin takarar Peter Obi"

Yan Kwankwasiyya.
Daruruwan yan Kwankwasiyya a wurin taron yakin neman zaben NNPP Hoto: Saifullahi Hassan
Source: Facebook

Magoyan bayan Obi da Kwankwaso

Aminiya ta tattaro cewa 'yan Kwankwasiyya sun ce ikirarin Atiku ba gaskiya ba ne, suna mai cewa mutum biyu kacal ne ke da mabiyan da ke kaunarsu da zuciya a fadin kasar nan, Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso.

Mai magana da yawun Kwankwasiyya, Hon. Habib Mailemo, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da ya yi a tashar Trust TV.

Ya ce mabiyan da Obi da Kwankwaso ke da su ba kudi aka ba su ba, sai dai sun samu irin wannan soyayya ne sakamakon yakinin jama’a da kwarewar shugabancin da suka nuna a baya.

“Peter Obi da jagorana, Alhaji Rabiu Musa Kwankwaso, su ne kadai ke da mabiyan da ba a sayensu da kudi. Jama’a sun yarda da su ne saboda kwarewarsu da irin ayyukan da suka yi,” in ji shi.

Kwankwasiyya ta ja hankalin 'yan ADC

Ya kara da cewa ya kamata tattaunawar siyasa a ADC ta karkata daga batun wanda ya fi karfi zuwa ga yadda za a ceto Najeriya daga halin da take ciki.

Kara karanta wannan

Dangote ya je Amurka, ya fadi yadda ake amfani da karfi don hana Afrika cigaba

A cewarsa, shiga hadakar jam’iyyun adawa da Kwankwaso ya yi na da manufa guda ne kawai, watau taimakawa wajen ceto kasar nan.

“Jagorana ya bayyana karara cewa ya shiga wannan hadaka saboda yana son bayar da gudunmawa wajen ceto Najeriya,” in ji shi.

Kwatanta Atiku da Kwankwaso

Da yake mayar da martani kan batun wanda ya fi tasirin siyasa a Arewa, Mailemo ya amince cewa Atiku ya dade yana siyasa, amma ya ce nasarorin da ya samu a baya sun dogara ne da goyon bayan jam’iyya da manyan ‘yan siyasa.

“Gaskiya ne Atiku ya taba takara sau da dama, musamman a PDP inda yake da goyon bayan gwamnoni da tsarin jam’iyya mai karfi. Amma ba zai iya danganta kuri’un da ya samu da karfinsa na kashin kai kadai ba,” in ji shi.
Atiku da Kwankwaso.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso Hoto: Atiku Abubakar
Source: Facebook
Ya jaddada cewa bambancin da ke akwai shi ne, Obi da Kwankwaso sun gina tasirinsu ne da kansu ba tare da dogaro da manyan tsare-tsaren jam’iyya ba.

A karshe, ya ce idan ana son a yi kwatance mai adalci da Atiku, dole ne a gwada shi a irin yanayin da bai samu cikakken goyon bayan manyan ‘yan siyasa ba.

Kara karanta wannan

Iran ta amince da bukatar Amurka, ta canza shawara kan batun kera makamin nukiliya

Atiku ya kare kansa daga cin hanci

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiki Abubakar, ya kare kansa kan yawan danganta shi da zargin cin hanci da rashawa da ake yi.

Atiku ya bayyana cewa Olusegun Obasanjo, ya taɓa ba da izinin kafa wani kwamiti domin bincikarsa lokacin da yake kan mulki amma ba a iya gano komai ba.

Ya ci gaba da cewa zarge-zargen cin hanci da rashawa da suka biyo shi tsawon shekaru sun samo asali ne daga siyasa maimakon kwararan shaidu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262