Gwamnati Ta Gano Yadda ‘Yan Ta’adda Suke Amfani da Sunan Mata Su Samu Kudi

Gwamnati Ta Gano Yadda ‘Yan Ta’adda Suke Amfani da Sunan Mata Su Samu Kudi

  • Hukumar NFIU ta gano yadda kungiyoyi irinsu ISWAP suke samun kudi kuma su kashe ba tare da an gane ba
  • 'Yan ta'adda suna amfani da sunayen mata da lambobin wayar mamata wajen bude asusun banki a Najeriya
  • An binciko yadda ake aiki da kafofin sadarwa wajen tara tallafin kudi a PayPal ko bankuna daga kasashen waje

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abuja - Hukumar NFIU ta bankado sabababbin hanyoyin da ‘yan ta’adda suke cigaba da amfani da su domin samun kudin yin barna.

‘Yan ta’adda sun rungumi harkar yin karo-karo daga wajen jama’a a gida da waje domin su samu kudin da suke addabar mutane da su.

Jami'an tsaro
Dakarun jami'an tsaro hadin-guiwa suna yakar 'yan ta'adda a Arewacin Najeriya Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

'Yan ta'adda na fakewa da sunan mata

Baya ga wannan, jaridar Punch ta rahoto cewa ‘yan ta’addan suna bude asusun banki da sunayen mata domin batar da kama.

Kara karanta wannan

‘Yan bindiga sun sace matar sarki, sun hau TikTok sun nemi a aiko masu N20m

Idan aka sa sunayen mata, ba a cika zargin komai ba. Amma maza suke amfani da asusun bankin ta ATM da manhajoji na waya.

Dabarar aiki da lambar wayar matattu a waya

Haka kuma jami’an NFIU sun gano suna amfani da lambar wayoyin mutanen da suka mutu domin cin karensu babu babbaka.

An kuma fahimci cewa da lambobin mamata ko layi masu rajista suke amfani wajen samun sakonni daga wajen bankuna cikin sauki.

Ta hanyar amfani da layin waya da aka yi wa rajista kafin a saida, ba a iya gano su ta hanyar amfani da lambobin fasahar BVN.

Ta haka sai ‘dan ta’adda ya cigaba da aiki da layin waya wato SIM da aka yi wa rajista a kasuwa da sunan wani mutumi can dabam.

Ko an tashi tura sakonni ko kudi kuwa, NFIU ta ce ana amfani da wani salon magana ne da ‘yan ta’addan kadai suke gane juna.

Kara karanta wannan

Abin tausayi: Yadda yan bindiga suka rika tashin mutane daga barci, su harbe su har lahira

Za a samu duka wadannan bayanan a rahoton karshen shekara na 2025 da NFIU ta fitar.

Ta ya 'yan ta'adda suke samun kudi?

Rahoton ya ce idan an tashi neman karo-karo, ana amfani da wayoyi sai a fake da neman gudunmuwar taimakon marasa karfi.

An ji cewa ana neman gudumuwar ne ta dandalin sada zumunta na Telagram ko Signal.

Wani lokaci kuma neman taimakon yana zuwa da rigar bunkasa harkar ilmi, a haka ‘yan ta’addan za su bi su sulale da kudi a asirce.

NFIU ta ce da wannan taimako ake lallaban mutane su bada gudumuwar $50 zuwa $500 ta PayPal ko dai wasu bankuna da aka sani.

Sojojin
Wasu Sojojin Najeriya a bakin aiki Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Idan an tashi dauke kudin da aka tara, ana amfani da asusun bankin ‘yan makaranta da kananan ‘yan kasuwa saboda gudun a ankara.

Da wadannan kudi aka saba sayen abubuwa irinsu keke, taki, babura, na’urorin zamani da sauransu domin yin ta’adi a jihohin Najeriya.

Masu daukar nauyin yan ta'adda

An rahoto Primate Elijah Ayodele ya ce wasu mutane biyar masu karfin iko a Najeriya suna daukar nauyin ta'addanci da garkuwa da mutane.

Kara karanta wannan

Sojojin Najeriya sun bindige dan bindiga har lahira a wani artabu da suka yi

Ya bukaci gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta gano wadannan mutane ta kuma kawar da su domin a samu dorewar zaman lafiya a Najeriya.

Fasto Ayodele ya gargadi gwamnati kan tattaunawa ko sulhu da 'yan ta'adda, ya ce hakan yana mayar da ta'addanci harkar kasuwanci ne kawai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng