Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Yi Babban Rashi, Hajiya Nana Asma'u Ta Riga Mu Gidan Gaskiya

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Yi Babban Rashi, Hajiya Nana Asma'u Ta Riga Mu Gidan Gaskiya

  • Gwamnan Sokoto Ahmed Aliyu ya jajanta wa Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar III kan rasuwar gwaggonsa, Hajiya Nana Asma’u
  • Rahotanni sun nuna cewa Nana Asma’u ta rasu ne ranar Talata da ta gabata tana da shekara 100 a duniya
  • Gwamna Aliyu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga iyalan gidan sarauta, Jihar Sokoto da Najeriya baki daya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sokoto, Nigeria - Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya jajanta wa Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, kan rasuwar matar mahaifinsa, Hajiya Nana Asma’u, wadda ta rasu ranar Talata tana da shekara 100.

Gwamnan ya kai ziyarar ta’aziyya ga Sarkin Musulmi a fadarsa da ke Sokoto, inda ya bayyana rasuwar marigayiyar a matsayin babban rashi ga gidan sarauta, Jihar Sokoto da ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Gwamna a Najeriya ya kamu da rashin lafiya har ya gaza fitowa aiki? Gaskiya ta bayyana

Sarkin Musulmi.
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III lokacin da ya karbi bakuncin tawagar Gwamna Ahmed Aliyu a fadarsa da ke Sokoto Hoto: @bellotsoho
Source: Twitter

Gwamna Aliyu ya ce an yi babban rashi

A rahoton Daily Trust, Ahmed Aliyu ya ce Nana Asma’u ta taka muhimmiyar rawa ta uwa a cikin gidan sarauta, yana mai cewa rasuwarta ta haifar da giɓin da zai yi wuya a cike.

“Rasuwar Nana Asma’u haƙiƙa wani babban rashi ne,” in ji gwamnan.

Ya roƙi Sarkin Musulmi da sauran ’yan uwa su karɓi rasuwar a matsayin ƙaddarar Allah Maɗaukaki, tare da addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayiyar kura-kuranta, Ya shigar da ita Aljanna.

Sarkin Musulmi ya gode wa gwamna

A nasa martanin, Sarkin Musulmi ya gode wa Gwamna Aliyu bisa ziyarar ta’aziyyar da ya kai masa, tare da yi masa addu’ar Allah Ya saka masa da alheri mai yawa.

“Muna addu’ar Allah Ya ba ka tsawon rai domin ka ci gaba da yi wa al'umma hidima,” in ji Sarkin Musulmi.

Gwamnan ya samu rakiyar Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko; shugaban APC na jihar, Haruna Adiya; ’yan majalisun dokoki; kwamishinoni; hadimai da sauran abokan siyasar sa.

Kara karanta wannan

'Yan ɗariƙa a Katsina sun tsaida wa mabiya waɗanda za su zaɓa a 2027

Malam Bashiru Gidan Kanawa ya jagoranci addu’o’i na musamman domin Allah Ya jiƙan Nana Asma’u da sauran waɗanda suka riga mu gidan gaskiya.

Gwamna ya ziyarci gidaje don ta'aziyya

Gwamnan ya kuma ziyarci wasu iyalan da suka yi rashin ’yan uwansu a cikin birnin Sokoto, ciki har da iyalan Abdullahi Kafinta na Rungumi, wanda ya rasu yana da shekara 80.

Srkin Musulmi
Gwamna Ahmed Aliyu lokacin da yake mika sakon ta'aziyya a fadar Sarkin Musulmi Hoto: @bellotsoho
Source: Twitter

Sauran iyalan da gwamnan ya ziyarta sun haɗa da na Aisha Umar, mai shekara 87; Abubakar Abdulraheem; Alhaji Garba Shugaba, mai shekara 85; Ahmad Mode na Gagi; da marigayi Aliyu Musa Mana na Mana.

An yi addu’a a dukkan gidajen da gwamnan ya ziyarta domin Allah Ya jiƙan mamatan.

Sarkin Musulmi ya yi ta'aziyyar Sarkin Gumel

Kun ji cewa Sarkin Musulmi ya mika sakon ta'aziyya bisa rasuwar Mai martaba Sarkin Gumel, Dr. Ahmed Muhammad Sani II, CON.

Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar ya ce raasuwar basaraken babban rashi ne ga masarautar Gumel, Jigawa da daukacin al'ummar Musulmi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262