Yaki da ta'addanci a Najeriya
Dan takarar gwamnan Bauchi. Shehu Buba Umar, ya mika kansa ga hukumomin tsaro domin bincike kan zargin da ake masa na hannu a ayyukan ta'addanci da daukar nauyinsu.
Rundunar ’yan sandan jihar Kebbi, tare da haɗin gwiwar sojoji, ta ce sun kashe ’yan bindiga da dama a dajin Gumki da ke Kangiwa, ƙaramar hukumar Arewa ta jihar.
Aƙalla fasinjoji tara ne aka kashe bayan wasu ‘yan bindiga sun buɗe wa wata motar haya wuta a mahadar tituna ta Dungus Junction da ke ƙauyen Kuru a jihar Filato.
Bayan Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) ta yi gargadi, Ƙungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) da al’ummar Musulmi sun ɗauki matakan hana yiwuwar kai hare-hare.
Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya kare Sanata Shehu Buba Umar zargin da ake yi masa na alaka da ta'addanci inda ya ce yaba masa kan kokarin da yake yi.
Kungiyar HURIWA ta bukaci Gwamnan Benue Hyacinth Alia ya yi murabus, tare da rokon Tinubu ya karfafa tsaro bayan sabon hari da ya kashe mutane 11.
Kasar Amurka ta bai wa Rundunar Sojin Sama ta Najeriya kayan aikin soja domin taimakawa ƙasar wajen yaƙi da ta’addanci a musamman Arewacin Najeriya.
Sanata Shehu Sani ya kalubalanci ’yan Arewa masu sukar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan matsalar rashin tsaron da ta addabi Najeriya, ya tuna Buhari.
Rundunar sojojin Najeriya ta naɗa Manjo Janar Ibikunle Ademola Ajose sabon kwamandan Operation Hadin Kai domin jagorantar yaƙi da Boko Haram da ISWAP.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari