Yan bindiga
'Yan bindiga dauke da makamai sun farmaki wasu kauyukan jihar Benue. 'Yan bindigan sun hallaka mutane tare da raunata wasu da dama yayin harin da suka kai.
Iyalan shugaban karamar hukumar Bungudu sun bayyana yadda 'yan bindiga suka mamaye gidansa, suka kashe mutane hudu sannan suka yi garkuwa da shi.
Sarkin Potiskum ya ce amfani da ƙarfin soja kaɗai ba zai kawo ƙarshen rashin tsaro a Najeriya ba, yana mai kira ga gwamnati ta magance talauci da rashin adalci.
'Yan bindiga sun nemi Naira miliyan 200 domin sakin alkalin Babbar Kotun jihar Kebbi, yayin da 'yan sanda ke ci gaba da ƙoƙarin ceto shi daga hannunsu.
A labarin nan, za a ji cewa rundunar tsaron kasar nan ta kara samun gagarumar nasara wajen kakkabe ayyukan yan bindiga da suka kai hari jihar Katsina.
Sanata Adams Oshiomhole ya ce jami'an tsaro su riƙa harbin masu ɗauke da makamai nan take, yana mai cewa rashin tsaro ne babban ƙalubalen gwamnatin Tinubu.
Akalla mutum 30, ciki har da yara takwas, sun mutu bayan 'yan ta'adda sun kai hari ƙauyen Naridon a Kaduna, inda suka ƙona gidaje da shaguna tare da jikkata wasu.
Tsohon jami’in DSS, Dennis Amachree, ya zargi gwamnatin marigayi Muhammadu Buhari da sakaci da rashin tsaro, cin hanci da biyan kuɗin fansa ga masu garkuwa.
‘Yan bindiga dauke da manyan makamai kuma sanye da kayan sojoji sun kashe mutane huɗu tare da jikkata wasu a harin da suka kai Unguwan Lalle a jihar Sokoto.
Yan bindiga
Samu kari