Yan ta'adda
Dakarun sojojin Najeriya sun cafke wani mutum da ake zargi da alaka da ISWAP a jihar Borno bayan gano hotonsa tare da wasu dauke da bindigogin AK-47.
Yan bindiga a Jihar Niger sun saki yara 48 da suka yi garkuwa da su har tsawon makonni uku bayan an biya kudi, inda a yanzu suka koma gida lafiya gaban iyayensu.
’Yan bindiga sun kashe Hakimin Galla, Alhaji Ahmed Yusuf, a Niger bayan ya yi musu gargadi, yayin da Gwamna Bago ya nemi a gurfanar da waɗanda suka aikata laifin.
Gwamnan Benue, Hyacinth Alia ya ce haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a Kwande na ƙara rashin tsaro, tare da yin kira ga al’umma su kare filayensu.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya umarci jami’an tsaro su kaddamar da aikin ceton masu ibada da aka yi garkuwa da su yayin sallar Juma’a a Jihar Neja.
Hukumar NFIU ta toni asirin yadda 'yan ta'adda ke yin amfani da asusun banki na matattun mutane, mata, da kafofin tara tallafi na intanet wajen tura kudi.
'Yan bindiga dauke da makami sun kai hari fadar basaraken Finima a jihar Rivers, inda HRH Dagogo Brown ya tsira, yayin da 'yan sanda suka kama mutum daya.
Rikici ya barke tsakanin kungiyoyin Boko Haram da ISWAP a Dajin Sambisa, inda aka ruwaito kashe mayaka da kuma mika wuya da wasu ‘yan JAS suka yi.
Dan majalisar Amurka Chris Smith ya zargi gwamnatin Najeriya da gazawa wajen kare 'yan kasa bayan sabbin hare-haren da suka kashe mutane a Plateau.
Yan ta'adda
Samu kari