'A Baya, Ina Goyon bayan Cire Tallafi': Atiku Ya Fadi dalilin Sauya Tunani kan Lamarin
- Atiku Abubakar ya sauya matsayinsa kan tallafin man fetur, inda ya ce zai dawo da shi idan aka zabe shi shugaban Najeriya a 2027
- Mai magana da yawunsa, Paul Ibe, ya kare matakin, yana cewa shugaba mai tausayi ya kamata ya sake duba manufofin da suke jefa jama'a cikin wahala
- Ibe ya ce shirin Atiku zai rage farashin tace man fetur a cikin gida, wanda zai saukaka sufuri, noma, masana'antu da sauran harkokin tattalin arziki
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi magana kan shirin dawo da tallafin mai a Najeriya.
Atiku ya tabbatar da cewa idan Allah ya ba shi nasara a zaben 2027 zai dawo da tallafin da Bola Tinubi ya cire.

Source: Twitter
Mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya fadi dalilin sauya tunanin Atiku a shafinsa na X.
Atiku ya fadi dalilin shirin dawo da tallafi
Ibe ya ce shugaba ya kamata ya kasance mai shirya sake duba wata manufa idan aiwatar da ita ya jefa 'yan kasa cikin wahala.
Atiku, wanda yanzu yake wakiltar ADC, a matsayin dan takarar shugaban kasa na 2027, ya ce zai dawo da tallafin man fetur
Ya ce cire tallafin ya kara matsin tattalin arziki ga 'yan Najeriya, ba tare da isasshen tabbacin cewa an yi amfani da kudaden da aka samu ba
Ya kuma tambayi abin da ya faru da kudaden da gwamnati ta samu bayan cire tallafin, musamman ko an kashe su wajen inganta kiwon lafiya
Atiku ya amince cewa a baya ya goyi bayan cire tallafin man fetur, amma ya ce sakamakon manufar ya sa ya sake duba matsayinsa.
Sabon matsayar Atiku ya jawo sabuwar takaddama da fadar shugaban kasa, wadda ta zarge shi da sauya matsayinsa saboda dalilan siyasa.

Source: Twitter
Atiku ya yi martani ga fadar shugaban kasa
Da yake mayar da martani, Ibe ya ce bai kamata a soki Atiku ba saboda ya sake tunanin matsayar da ya dauka a 2023 ba
Ibe ya amince cewa Atiku ya goyi bayan cire tallafin a yakin neman zaben 2023, amma ya ce sauya matsaya ba lallai ne ya zama munafurci ba
Ya ce abin da ya fi muhimmanci shi ne ko manufar ta inganta rayuwar talakawa, da kuma ko kudaden da aka samu sun amfani jama'a yadda ya kamata
Ibe ya ce ya kamata a duba ko kudaden sun inganta sufuri, kiwon lafiya, ilimi, samar da ayyukan yi da kuma tallafin jin dadin jama'a
Tinubu ya soki Atiku kan shirin dawo da tallafi
Mun ba ku labarin cewa Fadar Shugaban Ƙasa ta soki Atiku Abubakar kan alkawarinsa na dawo da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓe a 2027.
Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Sunday Dare, ya ce shirin Atiku yaudara ne da zai iya kawo cikas ga tattalin arziki.
Atiku ya ce bai taɓa adawa da cire tallafin ba, amma ya tambayi yadda aka kashe kuɗin da aka samu bayan cire tallafin.
Asali: Legit.ng


