Matsin tattalin arziki
Alkaluman DMO sun nuna cewa kudin da aka biyo Najeriya a matsayin bashi sun tabo Naira tiriliyan 159 zuwa karshen 2025, idan aka raba nana bin kowa N724000.
Cibiyar kididdiga ta kasa, NBS ta sanar da cewa farashin kayan abinci ya tashi da kashi 15.38 a watan Maris na 2026. Tashin farashin ya shafi Gombe, Zamfara, Taraba.
Attajirin Najeriya, Alhaji Aliko Dangote ya shiga cikin jerin mutane 100 mafi tasiri a duniya da mujallar Time ta fitar a 2026. Donald Trump na cikin mutanen.
Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa ba za ta maido tallafin man fetur duk da tashin farashin man fetur a kasuwanni. Wale Edun ya ce za a tallafawa talaka.
Kasar Musulunci ta Iran ta bayyana cewa a binciken farko da ta yi, ta gano cewa ta yi asarar akalla Dala biliyan 270 a yakinta da hadin gwiwar Amurka da Isra'ila.
Miliyoyin yan Najeriya da ke fatan samun sauki idan sulhun Amurka da Iran ya tabbata sun samu koma baya, ana hasashen fetur zai iya iara tsada fiye da baya.
Shugaba Bola Tinubu ya umarci jami’an tattalin arziki su samar da matakan rage radadin da rikicin Gabas Ta Tsakiya ke jawo wa rayuwar ‘yan Najeriya.
Kungiyar kwadaho ta TUC ta bayyana cewa alamu sun nuna farashin litar fetur za ta iya haura N2000 a Najeriya, wanda hakan babbar matsala ce ga talakawa.
Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya musanta cewa Najeriya na shirin durƙushe, inda ya jero nasarorin tsaro da tattalin arziki da aka samu a gwamnatin Tinubu.
Matsin tattalin arziki
Samu kari