Jihar Legas
Mijin tsohuwar Ministar Kuɗi, Kemi Adeosun, Anthony Adeosun, ya rasu yana da shekara 62 a duniya, kamar yadda iyalansa suka sanar a cikin wata sanarwa.
Matatar Dangote da ke jihar Legas ta rage farashin fetur zuwa N1,165 kan kowace lita daga N1,215, sannan ta sauke farashin dizal zuwa N1,570 a Najeriya.
Hukumar FAAN ta tabbatar da tashin gobara a wani bangare na filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Legas. Rahotanni sun ce ba a samu asarar rai ba.
Alkalin Alkalai a Najeriya ta haramta amfani da lakabin “Barrister” a mu’amalar hukuma da Kotun Koli, tana mai cewa bai dace da ƙa’idojin ƙwarewar aiki ba.
Mutuwar Emmanuel Abiodun Adewale Alogbo, shugaban cocin Cherubim and Seraphim Movement na duniya baki ɗaya, ta jawo saƙonnin ta'aziyya daga al'ummar Kiristoci.
Sheikh Surajudeen Akanni, wanda aka fi sani da Arizukuna, ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya, yayin da malamai da iyalansa suka bayyana alhininsu.
Bidiyon da ya nuna kwamishinan yan sanda a Lagos, Tijani Fatai a taron City Boy Movement ya haddasa cece-kuce, yayin da NDC ta bukaci a dauki mataki kan halartarsa.
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta sanar da rasuwar tsohon AIG Adeleke Taiwo Olatunde da CP Hassan Saleh Gwani tare da yabawa gudummawar da suka bayar.
Takardun bincike sun bayyana yadda ake zargin wasu jami'an soja suka tsara shirin kifar da gwamnatin Tinubu, tare da raba ayyuka da tsara dabarun aiwatarwa.
Jihar Legas
Samu kari