Babbar Magana: Kotu Ta Ƙwace Naira Miliyan 150 na Wani 'Dan Majalisar Tarayya a Najeriya
- Babbar Kotun Tarayya ta ba da umarnin kwace Naira miliyan 150 da ake dangantawa da dan Majalisar wakilai, Hon. Nicholas Mutu
- Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ta ce kudin sun samo asali ne daga haramtattun ayyukan dan Majalisar
- Bisa haka ne EFCC ta gabatar da bukatar kwace kudin gaba daya, kuma kotun ta amince da hakan bisa hujjojin da aka gabatar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da umarnin kwace Naira miliyan 150 da ake dangantawa da dan majalisar wakilai, Nicholas Mutu, tare da mika kudin ga Gwamnati Najeriya.
Hon. Mutu, wanda ke wakiltar mazabar Bomadi/Patani ta Jihar Delta a majalisar wakilai, ya sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa APC a tsakiyar shekarar 2025.

Source: Facebook
EFCC ta tabbatar da hukuncin kotu
Hukumar Yaki da Masu Yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta'annati (EFCC) ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X ranar Juma'a, 3 ga Yulin 2026.
A cewar hukumar, Mai Shari'a Joyce Abdulmalik ta yanke hukuncin ne bayan ta amince da bukatar EFCC na kwace kudin har abada.
Kotun ta ce bayan nazarin bukatun da aka gabatar da kuma bayanan rantsuwa daga lauyoyin ɗan majalisa da kamfaninsa, Airworld Technologies Ltd, ta gano cewa bukatar EFCC ta dace da doka.
Kotun ta yanke cewa kudin Naira miliyan 150 da Mutu ya mayar sun kasance kudaden da aka samu ta haramtacciyar hanya, saboda haka ta ba da umarnin mika su ga gwamnatin tarayya.
EFCC ta bayyana hujjojinta
EFCC ta ce ta gabatar da bukatar ne bisa tanadin Sashe na 44(2) na Kundin Tsarin Mulkin 1999 da kuma Sashe na 17 na Dokar Advance Fee Fraud and Other Related Offences ta shekarar 2006.

Kara karanta wannan
An mika wa Tinubu rahoto kan kara wa shugaban kasa da masu mukaman siyasa albashi
Hukumar ta kuma tuna cewa tun farko kotun ta bayar da umarnin kwace kudin na wucin gadi tare da umartar a wallafa sanarwar a wata jarida ta kasa.
Ta ce babu wanda ya gabatar da gamsasshiyar hujja da za ta hana a kwace kudin har abada.
Abin da binciken EFCC ya gano
A cewar EFCC, bincikenta ya nuna cewa Nicholas Mutu ya karbi cin hanci da ya kai Naira miliyan 400,159,689.63 daga kamfanin Starline Consultancy Services, wanda ke ba Hukumar Raya Yankin Neja Delta (NDDC) shawara.
Hukumar ta ce hakan ya faru ne lokacin da dan Majalisar ke shugaban kwamitin majalisar wakilai mai kula da NDDC.

Source: Twitter
EFCC ta ce kudaden sun rika shiga asusun kamfanonin Airworld Technologies Ltd da Oyien Homes Ltd a Heritage Bank, inda aka yi zargin an halasta su.
Ta ce ɗan majalisar wakilan shi ne babban mai hannun jari kuma darakta a kamfanonin, yayin da matarsa da sauran 'yan uwansa ke rike da sauran hannayen jari.
EFCC na bincike kan gyaran matatun fetur
A wani labarin, kun ji cewa EFCC ta gurfanar da tsofaffin shugabannin matatun man fetur na Fatakwal da Warri gaban kotu.
Hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawar ta gurfabar da mutanen biyu ne kan zargin halasta kudaden haram da suka shafi kudaden gyaran matatun mai na Najeriya.
Wannan mataki na zuwa ne a cikin binciken da EFCC ke yi kan shirin gyaran manyan matatun man fetur na Najeriya da aka kashe makudan kudade a kai.
Asali: Legit.ng

