Yaki da rashawa a Najeriya
EFCC ta gurfanar da wasu tsofaffin shugabannin matatun Port Harcourt da Warri kan zargin wanke kudin haram da karkatar da kudaden gyaran matatun mai.
ICPC ta gurfanar da Nasir El-Rufai da wasu mutane biyar kan tuhume-tuhume 11 da suka shafi zargin cin hanci da kwangilar CCTV ta N8.68bn a Kaduna.
Babbar kotun jihar Kano ta dage shari'ar da gwamnatik Kano ke tuhumar tsohon shugaban APC, Abdullahi Ganduje, matarsa da dansa da karkatar da kudin jama'a.
Babbar kotun tarayya da ke Kaduna ta dage sauraron shari’ar tsohon gwamna Nasir El-Rufai bayan wasu da ake kara tare da shi sun kasa zuwa zaman kotun.
Shugaban EFCC na kasa, Ola Olukoyede ya ce kudin da wasu yan takara ke kashewa wajen neman mulki na taimaka wa wajen karuwar cin hanci da rashawa.
A labarin nan, za a ji cewa wasu takardu da aka gabatar a gaban kotu sun nuna dabarun da tsohon Akanta Janar Dakta Sa'idu Abubakar ya bi, ya kwashi kuɗi a Bauchi.
Hukumar EFCC ta gurfanar da wani boka da matarsa a kotun tarayya da ke Ado-Ekiti bisa zargin damfarar kusan Naira biliyan biyu daga wata bazawara.
EFCC ta kai tsohon ministan wutar lantarki, Saleh Mamman, gidan yari na Kuje bayan kotu ta yanke masa hukuncin shekaru 75 kan laifuffukan rashawa.
ADC ta zargi hukumar ICPC da hana shugabanninta ganin Nasir El-Rufai tare da cewa ana amfani da hukumomi wajen tsoratar da ‘yan adawa a NAjeriya.
Yaki da rashawa a Najeriya
Samu kari