Duk da Tatsar N10m daga Al'umma, Ƴan Bindiga Sun Kona Makarantar Firamare Kurmus
- Yan bindiga sun kona makarantar firamare bayan sun karɓi harajin Naira miliyan 10 da suka tilasta al’ummomin yankin
- Mazauna yankin sun ce maharan sun fito daga dajin Kainji, suka kai hari hedikwatar gundumar tare da lalata makarantar
- A wani harin kuma, an kashe mutum ɗaya yayin da aka sace wani a hare-haren da aka kai a wasu kauyuka
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Minna, Niger - Majiyoyi sun ruwaito cewa 'yan bindiga sun ƙone wata makarantar firamare da ke garin Dekara a ƙaramar hukumar Borgu ta Niger.
Maharan sun ɗauki wannan matakin ne duk da cewa sun karɓi harajin Naira miliyan 10 daga al’ummomin yankin.

Source: Original
Mazauna yankin sun shaida wa Daily Trust cewa maharan sun banka wa makarantar firamare ta 'Central', Dekara wuta ne yayin wani hari da suka kai garin.

Kara karanta wannan
'Yaran jagoran 'yan bindigan da suka sace Janar sun sake sabon ta'addanci a Katsina
Abin da mazauna yankin ke cewa
Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya ce 'yan bindigar sun fito ne daga dajin Kainji kafin su mamaye al’ummar.
A cewarsa, ƙauyuka da al’ummomin gundumar Dekara sun haɗa kuɗi tare domin biyan Naira miliyan 10 da 'yan bindigar suka nema bayan sun yi barazanar kai hari.
Ya bayyana cewa an biya kuɗin ne bayan maharan sun yi alkawarin barin mazauna yankin su ci gaba da zama cikin ƙauyukansu ba tare da ƙarin hare-hare ba.
“'Yan bindigar sun kakaba mana harajin Naira miliyan 10, mun biya saboda sun yi barazanar kai mana hari idan muka ƙi biyan kuɗin.
“Amma duk da sun karɓi kuɗin, sun sake kai hari hedikwatar gundumar tare da ƙona makarantar firamare."
- in ji mazaunin yankin

Source: Twitter
Matsalolin da jihar Niger ke ciki
Jihar Niger na daga cikin jihohin da ke fama da hare-haren yan bindiga wanda ya jawo asarar rayuka da dukiyoyin al'umma, cewar rahoton Premium Times.
Al'umma, masu ruwa da tsaki da masu fashin baki kan harkokin yau da kullum suna nuna damuwa kan ci gaba da kashe mutane da ake yi ba kakkautawa inda suka bukaci hukumomi su kawo karshen abin da ke faruwa.
Har zuwa lokacin tattara wannan rahoton, ba a samu jin tabakin kakakin rundunar yan sandan jihar ba domin yin karin haske.
Mai magana da yawun rundunar, SP Wasiu Abiodun, bai amsa kiran waya ba, haka kuma bai mayar da martani ga saƙon tes da aka aika masa ba.
Yan bindiga sun yi wa mutane wa'azi
Mun ba ku labarin cewa wasu ‘yan ta'adda masu ikirarin jihadi sun shiga Neja tare da tara mazauna Zugurma domin gabatar da wani wa’azi mai cike da barazana.
Mazauna yankin Zugurma sun ce mayakan sun iso garin da babura kusan 30 sanye da kayan sojoji da rawani kafin su rarraba kansu domin yin wa'azi.
Ana zargin cewa 'yan ta'addar suna karkashin ƙungiyar Lakurawa ne, wacce masu nazarin tsaro ke danganta ta da ƙungiyoyin jihadi.
Asali: Legit.ng
