Jihar Niger
Mazauna yankin karamar hukumar Shiroro a jihar Neja sun ce wadanda suka mutu a harin yan bindiga na ranar Talata sun hada da jami'an tsaro da fararen hula.
Wani mutum mai suna Hamisu Abdullahi mai shekaru 38 ya shiga hannu bayan ya yi ihu “ba ruwa, ba wuta” lokacin ziyarar gwamnan Niger a Suleja da ke jihar.
'Yan ta'addan Boko Haram sun tayar da wata gada mai muhimmanci a jihar Neja, lamarin da ya datse hanyoyin kasuwanci tsakanin Najeriya da jamhuriyar Benin.
A labarin nan, za a ji cewa wasu manyan matsaloli sun fara yi wa ƴan ta'adda a jihohin Neja da Zamfara dabaibayi, suna kwance ba magani ballantana su nemi lafiya.
Babban hafsan tsaron kasa (CDS), Janar Olufemi Olatubosun Oluyede, ya kaddamar da rundunar Operation Savannah Shield, da za ta fattaki 'yan ta'adda a Kwara Neja.
Kungiyar Kiristocci a Najeriya CAN ta jihar Niger ta ƙara yin ƙorafi kan kudirin dokar Hisbah, ta ce zai haifar da wariya ga Kiristoci da kawo rabuwar kai a jihar.
Wasu tsagerun yan bindiga da suka kai 200 sun shiga garuruwa uku a yankin karamar hukumar Borgu ana shirin sallar asubah, sun kashe gomman mutane yau Asabar.
Hafsan tsaron Najeriya, Janar Oluyede ya sanar da cewa za a tura dakaru na musamman zuwa Kwara da Niger. Ya nemi a ƙarfafa ƴan sanda da jami'an NSCDC.
Kamfanin TCN ya sanar da gyaran taransifomomi a Minna da Suleja yau 10 ga Fabrairu, 2026. Za a samu tsaikon wutar lantarki a sassa da dama har sai an kammala gyara.
Jihar Niger
Samu kari