INEC Ta Mika Takarda ga 'Yan Takarar da Suka Lashe Zaben Cike Gurbi a Kano da Wasu Jihohi 5
- Hukumar zabe INEC ta mika takardun shaidar nasara ga wadanda suka lashe zabukan cike gurbi da aka gudanar ranar Asabar
- Zabukan sun gudana a mazabun sanatoci, Majalisar Wakilai da Majalisar Dokokin Jiha a Kano, Kebbi da wasu jihohi hudu
- Hukumar ta ce za ta kuma mika takardar shaidar nasara ga zababben gwamnan Ekiti da wanda ya lashe zaben mazabar Zuru a Kebbi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) ta mika takardun shaidar nasara ga wadanda suka lashe zabukan cike gurbi da aka gudanar ranar 20 ga watan Yuni, 2026, a jihohi shida na kasar nan.
Zabukan sun shafi kujerun Sanata a Enugu, Nasarawa ta Arewa, Ondo ta Kudu da Rivers ta Kudu maso Gabas, kujerar Majalisar Wakilai ta Dawakin Kudu/Warawa a Kano, da kujerar mazabar Zuru ta Majalisar Dokokin jihar Kebbi.

Source: Facebook
INEC ta tabbatar da mika takardun shaidar nasara da wadanda suka lashe zabukan wadannan mazabu a wata sanarwa da ta wallafa a shafin X yau Talata.
INEC ta taya zaɓaɓɓun yan takara murna
Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, wanda Kwamishinar Hukumar ta Kasa mai kula da jihar Rivers, May Agbamuche-Mbu, ta wakilta, ya halarci taron mika takardun shaidar nasarar.
Da take jawabi, Agbamuche-Mbu ta taya wadanda suka yi nasara murna tare da jaddada muhimmancin wakiltar al’ummarsu yadda ya kamata.
Ta ce babban nauyin da ke kansu yanzu shi ne tabbatar da cewa sun yi wa mutanen da suka zabe su aiki cikin gaskiya da rikon amana.
“Abu mafi muhimmanci shi ne ku wakilci al’ummarku yadda ya kamata tare da sauke nauyin da aka dora muku,” in ji ta.
Za a mika takarda ga gwamnan Ekiti
Agbamuche-Mbu ta kuma bayyana cewa hukumar INEC za ta mika takardar shaidar nasara ga zabaɓɓen gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji a ofishint da ke birnin Ado-Ekiti.
Hakazalika, ta ce za a mika takardar shaidar nasara ga wanda ya lashe zaben mazabar Zuru ta Majalisar Dokokin jihar Kebbi a Birnin Kebbi.

Source: Facebook
Kwamishinonin INEC da ke wakiltar jihohin da aka gudanar da zabukan cike gurbi sun mika takardun shaidar nasarar ga yan takarar da suka lashe zabe.
Mika takardun ya tabbatar da su a hukumance a matsayin wadanda suka lashe zabukan cike gurbin da aka gudanar a yankunansu daban-daban.
INEC ta fitar da alkaluman rijistar zabe
A wani rahoton, kun ji cewa hukumar INEC ta bayyana Kano a matsayin jihar da ta fi samun yawan sababbin masu rijistar kada kuri'a a fadin Najeriya.
Alkaluman da hukumar ta fitar sun nuna cewa mutum 321,921 ne suka kammala rajista ta yanar gizo, yayin da wasu 259,377 suka kammala rajista a cibiyoyin rajista.
Bayanan INEC sun nuna cewa jihar Kano ce ta fi kowace jiha yawan sababbin masu rajista da mutum 49,603 yayin da jihar Sokoto ta zo ta biyu da mutum 32,293, sai kuma Lagos ta kasance ta uku da mutum 27,294.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

