Bola Tinubu Ya Nada Tsohon VC a matsayin Shugaban Hukumar NUC ta Najeriya

Bola Tinubu Ya Nada Tsohon VC a matsayin Shugaban Hukumar NUC ta Najeriya

  • Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada tsohon shugaban jami'ar UNILAG, Farfesa Oluwatoyin Ogundipe, a matsayin shugaban hukumar NUC
  • Farfesa Ogundipe ya maye gurbin Olufemi Aina, wanda ya yi murabus kasa da shekara guda bayan nadinsa a mukamin
  • Gwamnatin tarayyya na fatan sabon shugaban NUC zai inganta tsarin jami'o'in Najeriya ta yadda za su yi gogayya a duniya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin tsohon shugaban Jami'ar Legas (UNILAG), Farfesa Oluwatoyin Ogundipe, a matsayin shugaban kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Jami'o'i ta Kasa (NUC).

Mai ba shugaban kasa shawara kan yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu yana rattaba hannu kan doka a Najeriya Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

A cewar sanarwar da Onanuga ya wallafa a shafinsa na X, Farfesa Ogundipe ya maye gurbin Olufemi Aina, wanda ya yi murabus daga mukaminsa kasa da shekara guda bayan nada shi.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta tanka da Peter Obi ya nemi Tinubu ya yi murabus

Aikin da aka dorawa shugaban NUC

Onanuga ya ce sabon shugaban zai jagoranci hukumar NUC da ke kula da tsarin jami'o'in Najeriya tare da mayar da hankali kan samar da kudade da kara wa jami'o'i gasa a matakin duniya.

Ya ce:

“An yi wannan nadin ne domin bunkasa inganci, fadada damar samun ilimi da kuma kare martabar bangaren ilimi a Najeriya.”

Tinubu ya fadi abin da yake tsammani

Sanarwar ta kara da cewa Shugaba Tinubu na sa ran Farfesa Ogundipe zai samar da nagartaccen shugabanci a NUC tare da tabbatar da ɗaga martabar jami'o'in Najeriya daidai da manufofin shirin Renewed Hope Agenda.

Farfesa Ogundipe ya rike kujerar shugaban Jami'ar Legas daga shekarar 2017 zuwa 2022, kamar yadda The Cable ta ruwaito.

Takaitaccen bayani kan Ogundupe

Ya samu digirin digirgir (PhD) a fannin ilimin tsirrai daga Jami'ar Obafemi Awolowo (OAU), sannan ya yi MBA a Jami'ar Legas.

Farfesan, wanda ya kware a fannin ilimin tsirrai, ya yi bincike kan fannoni da suka hada da,Molecular Plant Taxonomy, Biosystematics,Ethnobotany, Cytogenetics, Forensic Botany, da kare muhalli da albarkatun kasa.

Kara karanta wannan

Peter Obi ya bukaci Tinubu ya kwaikwayi Starmer wajen yin murabus daga mulki

Onanuga ya bayyana cewa malamin mai shekaru 66 a yanzu yana matsayin shugaban majalisar gudanarwa na Jami'ar Redeemer’s da ke Ede a jihar Osun.

Oluwatoyin Ogundipe
Sabon shugaban hukumar NUC ta kasa, Farfesa Oluwatoyin Ogundipe Hoto: @OfficialNUC
Source: Twitter

Har ila yau, Oluwatoyin Ogundipe mamba ne na kungiyoyi masu yawa na masana kimiyya, ciki har da, Nigerian Academy of Science, Linnaean Society of London da Royal Society of Biology

Nadin na daga cikin matakan da gwamnatin tarayya ke dauka domin karfafa tsarin ilimin jami'o'i da inganta nagartar ilimi a Najeriya.

Tinubu ya tsawaita wa'adin shugaban NCS

A wani rahoton, kun ji cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ƙara tsawaita wa’adin aikin shugaban Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS), Adewale Adeniyi, da watanni shida.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce sabon ƙarin wa’adin na watanni shida, wanda zai ƙare a watan Fabrairun 2027, zai ba Adeniyi damar ƙarfafa aiwatar da tsare-tsaren gwamnati tare da tabbatar da sauyin shugabanci cikin tsari.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262