Gwamnatin tarayyar Najeriya
Sabon ministan wutar lantarki, Joseph Tegbe ya bayyana cewa matsalolin karancin wutar Najeriya suna da yawa, ba zai yiwu a magance su cikin dan lokaci ba.
Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC sun gargadi gwamnatin tarayya ta gaggauta samar da mafita kan matsalar tsaro da ke kara ta'azzafa a sassan kasar nan.
Gwamnatin tarayya ta hannun ma'aikatar kudi ta fara biyan 'yan kwangila na cikin gida basussukan da suka dade suna jira. An biya 'yan kwangila sama da 1,000.
Gwamnatin tarayya ta yi garambawul a tsarin kudin Imprest, wanda ake ba wasu jami'an gwamnatin kasar nan domin biyan wasu bukatunsu na yau da kullum.
Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume ya bayyana cewa yan Arewa maos Gabas za su saka wa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da kuri'insu bisa aikin titin Gombe zuwa Biu.
Majalisar Dinkin Duniya ta nuna damuwa kan sace dalibai a makarantu da dama a jihohin Oyo da Borno, ta nemi a gaggauta ceto su cikin koshin lafiya.
Shugaban jam'iyyar PRP na kasa, Hakeem Baba Ahmed ya nuna damuwa kam yadda matsalar tsaro ke kara yaduwa a fadin kasar nan, ya bukaci Tinubu ya yi murabus.
Kungiyar m'aikatan gwamnatin tarayya ta ce N100,000 ba ta dace da halin matsin tattalin arzikin da ma'aikata ke ciki ba, ta bai wa Shugaba Tinubu wa'adi.
Kungiyar kwadago ta NLC ta yi fatali da tayin N100,000 a matsayin mafi karancin albashin ma'aikata da gwamnoni suka yi, ta ce N1m ne ya dace da halin da ake ciki.
Gwamnatin tarayyar Najeriya
Samu kari