
Gwamnatin tarayyar Najeriya







Shugaban kasa Bola Tinubu ya nada mutane 11 mukamai a cikin kwanaki 15 na farkon watan Satumba. Daga cikinsu akwai Zacch Adedeji, mukaddashin shugaban FIRS.

A ranar 1 ga Oktoba Najeriya za ta cika shekara 63 da samun ‘yancin kai a hannun turawan Birtaniya. Kwamiti mai mutane 15 zai shirya bukukuwan da za ayi na bana.

Bola Ahmed Tinubu ya shiga gana wa yanzu haka da shugaban APC nanƙasa, Abdullahi Umar Ganduje da manyan shugabannin hukumomin tsaro na ƙasa a Abuja.

Bayan shafe fiye da sa'o'i 12 babu wuta a Najeriya, yanzu Kamfanin samar da wutar lantarki ya sanar da gyara wutar tare da dawo da ita, ya godewa jama'a da hakurinsu

Bayan shafe kusan shekara guda a Najeriya, an sake dauke wutar lantarki gaba daya a kasar a safiyar yau Alhamis 14 ga watan Satumba, kamar yadda kamfanin ya sanar.

Gwamnan Neja, Umar Bago, ya bayyana aniyarsa na fara gyara tituna a fadin jihar ciki harda titunan tarayya. Ya ce za su nemi a dawo da kudin da suka kashe daga baya.

Abubakar Momoh, ministan raya yankin Neja Delta a gwamnatin Tinubu ya gana da tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan da Asari Dakubo a birnin Abuja.

Gwamnatin tarayya ta bada aikin gyara hanyar Amanwozuzu-Uzoagba-Eziama-Orie-Amakohia a Imo. David Umahi ya ce 'dan kwangilar da ke aikin ya ji kunya.

A yau Bola Tinubu ya zauna da Gwamnatin UAE, an cire takunkumi a kan 'Yan Najeriya. Za a cigaba da zuwa Dubai bayan Bola Tinubu ya sa baki a rikicin da ya gada.
Gwamnatin tarayyar Najeriya
Samu kari