Bola Tinubu Ya Sake Tsawaita Wa'adin Shugaban Hukumar Kwastam Ta Najeriya
- Shugaba Bola Tinubu ya ƙara wa’adin aikin shugaban Hukumar Kwastam, Adewale Adeniyi, da watanni shida
- Adeniyi zai jagoranci ɗaga matsayin jami’an da suka cancanta tare da kula da ritayar waɗanda suka kai shekaru 60 ko suka yi shekaru 35 a aiki
- An naɗa shi shugaban Hukumar Kwastam a watan Yunin 2023, sannan aka tabbatar da shi a matsayin cikakken shugaba a Oktoba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ƙara tsawaita wa’adin aikin shugaban Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS), Adewale Adeniyi, da watanni shida.
Wannan mataki na zuwa ne yayin da wa'din shekara guda da Shugaba Bola Tinubu ya kara masa a bara ke dab da karewa.

Source: Facebook
Dalilin karawa shugaban kwastam wa'adi
Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Juma’a, 19 ga watan Yuni, 2026.
A cewar Bayo Onanuga, wa’adin da aka ƙara wa Adeniyi na shekara daya a watan Yulin 2025 zai kare ne a ranar 1 ga Agustan 2026.
Ya ce sabon ƙarin wa’adin na watanni shida, wanda zai ƙare a watan Fabrairun 2027, zai ba Adeniyi damar ƙarfafa aiwatar da tsare-tsaren gwamnati tare da tabbatar da sauyin shugabanci cikin tsari.
Ayyukan da ke gaban shugaban kwastam
Sanarwar ta ce a lokacin wannan ƙarin wa’adi, Adeniyi zai yi aiki tare da Hukumar Gudanarwar Kwastam domin tabbatar da ɗaga matsayin jami’an da suka cancanta zuwa mukamin Kwanturola na Kwastam.
Haka kuma zai kula da ritayar dole ga jami’an da suka kai shekaru 60 ko kuma waɗanda suka yi shekaru 35 suna aikin gwamnati.
Yadda ya shiga aikin Kwastam
Adeniyi ya shiga Hukumar Kwastam ta Najeriya ne bayan kammala karatunsa a Jami’ar Obafemi Awolowo a ƙarshen shekarun 1980.
Ya yi ta hawa matakan aiki har ya zama Mataimakin Kwanturola a shekarar 2012, sannan Kwanturola a 2017.
A shekarar 2020 ya zama Mataimakin Babban Kwanturola Janar, kafin a naɗa shi Mukaddashin Kwanturola Janar a watan Janairun 2023.
Daga bisani, Shugaba Tinubu ya naɗa shi Babban Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam a watan Yunin 2023.
Tinubu ya tabbatar da naɗinsa a 2023
A ranar 19 ga Oktoban 2023, Shugaba Tinubu ya tabbatar da Adeniyi a matsayin cikakken Babban Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam.
Kafin haka, yana riƙe da mukamin ne a matsayin mukaddashi bayan ya karɓi ragamar shugabancin hukumar daga tsohon shugaban Kwastam, Hameed Ali, a watan Yunin 2023.

Source: Twitter
Tun da farko, wa’adinsa zai ƙare ne a ranar 31 ga Agustan 2025 bayan cika shekaru 35 yana aiki, amma shugaban ƙasa ya ƙara masa shekara guda, wadda ake sa ran za ta ƙare a watan Agustan 2026.
Kwastam ta kawo tsarin gwajin kwaya
A wani labarin, kun ji cewa hukumar kwastam ta shirya yaki da matsalar ta'ammali da miyagun kwayoyi daga wajen jami'an da ke aiki a karkashinta.
Shugaban hukumar kwastam, Bashir Adewale Adeniyi, ya bayyana cewa ba za su lamunci ma'aikata na aiki a cikin yanayi mara kyau ba.
Ya umarci cewa a rika gudanar da gwajin miyagun kwayoyi ga sababbin ma’aikata da kuma jami’an da ke aiki a yanzu.
Asali: Legit.ng

